< Daniyel 2 >

1 A shekara ta biyu ta mulkinsa, Nebukadnezzar ya yi mafarkai; hankalinsa ya tashi har ya kāsa barci.
Amola ode aduna amoga Nebiuga: denese da hina bagade galu, e da simasia ba: i galu. Amo simasi amo ganodini e da da: i dioi galu. Amo da: i dioiba: le e da gola noga: le hame golai.
2 Sai sarki ya sa aka tattara masa masu sihiri da masu dabo da bokaye da masanan taurari domin su faɗi abin da ya yi mafarki a kai. Da suka shigo suka tsaya a gaban sarki,
Amaiba: le, e da bagade dawa: su dunu, nabi dunu, ba: la: lusu dunu amola wamuni dawa: su dunu amo simasia e ba: i, ea bai ema olelema: ne, ema misa: ne sia: i. Ilia da misini, amo hina bagade amo ea odagidili lelu.
3 sai ya ce musu, “Na yi mafarkin da ya dame ni kuma ina so in san me yake nufi.”
Amanoba, e amane sia: i, “Na simasi goega nina da da: i dioi bagade nabi. Amaiba: le, amo simasi ea bai, na dawa: mu hanai gala.”
4 Sai masanan taurarin suka amsa wa sarki da Arameyanci “Ran sarki yă daɗe! Ka faɗa wa bayinka mafarkin, mu kuma sai mu fassara.”
Ilia da hina bagadema amane sia: i, “Hina bagade! Di da eso huluane noga: le esalalalumu da defea. Dia simasi hou ninima adodole ima. Amalalu, amo ea bai ninia da dima olelemu,” amo simasi dawa: su dunu ilia amane sia: i.
5 Sai sarki ya amsa wa masanan taurarin ya ce, “Na mance da abin, idan ba ku tuno mini mafarkin, duk da fassararsa ba, to, za a daddatse ku gunduwa-gunduwa, a mai da gidajenku juji.
Amo sia: nababeba: le, hina bagade da ilima amane sia: i, “Na asigi dawa: su, na da hame afadenemu. Dilia na simasi ea hou amola bai gilisili nama adoma. Na dafawane dilima sia: sa, be dilia nama hame adosea, na da dadi gagui dunu ilima amane adomu. Dilia bogoma: ne, na da dilia emo amola lobo dagama: ne sia: mu. Amalu dilia diasu amolawane wadela: ma: ne sia: mu. Amalalu, amo diasu da doudafa agoai ba: mu.
6 Amma in har kuka faɗa mini mafarkina kuka kuma bayyana fassararsa, za ku sami lada mai girma. Saboda haka ku faɗa mini mafarkin da kuma fassararsa.”
Be dilia da na simasi ganodini sodoi liligi amo huluane amola simasi ea bai amola huluane noga: le olelesea, defea, na da liligi bagade dilima imunu amola dunu ilia dilima nodoma: ne sia: mu. Defea! Amaiba: le, simasi ea hou amola ea bai hedolowane olelema.
7 Sai suka sāke amsa masa suka ce, “Ran sarki yă daɗe, faɗa wa bayinka mafarkin, mu kuma za mu fassara shi.”
Amanoba, ilia dabe hina bagadema adole i, “Hina bagade! Di da dia simasi, amo ninima hidadea adodole ima. Amo nabalu bai ninia olelemu.”
8 Sai sarki ya amsa ya ce, “Na gane cewa kuna ƙoƙari ku ɓata lokaci ne kawai domin ku ga na manta da abin.
9 In ba ku faɗa mini mafarkin ba, akwai hukunci guda ɗaya kurum dominku. Kun haɗa baki domin ku faɗa mini munanan al’amura domin ku ruɗe ni har lokaci yă wuce. Sai ku faɗa mini mafarkin, ta haka kuwa zan sani za ku iya yi mini fassararsa.”
Amalalu, hina bagade da bu adole i, “Na dawa: dilia adodigisu hou na dawa: ! Dilia da simasi ea hou amola ea bai gilisili nama hame olelelalu, na da dili huluanema se defele imunu. Amo dawa: beba: le, dilia da gilisili sia: da: dawa: lalu, na asigi dawa: su afadenemusa: nama ogogosa. Hedolo! Simasi ea hou nama adoma. Amasea, dilia da simasi ea bai amola olelemusa: dawa: , amo na da dawa: mu galebe!” Nebiuga: denese da amane sia: i.
10 Sai masanan taurarin suka amsa wa sarki suka ce, “Babu wani mutum a duniyan nan da zai iya yin abin da sarki yake nema! Babu wani sarki mai daraja da girma wanda ya taɓa yin irin wannan tambaya ga masu sihiri ko masu dabo ko masanan taurari.
Hina bagade ea sia: i amo ilia nababeba: le, ilia bu dabe amane sia: i, “Dia dawa: mu hanai liligi olelemu da hamedei. Dunu afae osobo bagadega da amo olelemu hamedei galebe. Musa: amola wali, hina bagade eno da ea ba: la: lusu dunu, ea nabi dunu amola ea wamuni dawa: su dunu ilima agoaiwane adole ba: su hamedafa adole ba: i.
11 Abin da sarki yake nema yana da wuya matuƙa. Babu wani da zai iya bayyana wannan ga sarki sai dai alloli; kuma ba su zama tare da’yan adam.”
Hina bagade! Dia adoi amo da gasa bagadedafa ba: sa. Osobo bagade dunu da bu adole imunu da hamedei. ‘gode’ ilia fawane da amo adole imunusa: defele gala, be ‘gode’ ilia da osobo bagade dunu gilisisu ganodini hame esala.”
12 Wannan ya sa sarki ya fusata ƙwarai, ya ba da umarni a tafi da dukan masu hikima na Babilon a kashe su.
Hina bagade da amo sia: nababeba: le ougi bagadedafa ba: i. Amaiba: le, e da dadi gagui dunu ilia da bagade dawa: su dunu huluane Ba: bilone sogega esalebe, amo medole legema: ne sia: i dagoi.
13 Sai aka ba da dokar da za a kashe masu hikima, sa’an nan aka aika mutane su je su nemo Daniyel da abokansa domin a kashe su.
Amaiba: le, ea sia: ga ilia da bagade dawa: su dunu huluane medole legemusa: momagei. Amola ilia da Da: niele amola ea samalali medole legema: ne sia: i dagoi.
14 Sa’ad da Ariyok, shugaban ƙungiyar matsaran sarki, ya fita domin yă kashe masu hikima na Babilon, sai Daniyel ya yi masa magana cikin hikima da dabara.
Amalalu, Da: niele da A: lioge (e da hina bagade ea dadi gagui dunu bisilua galu. Hina bagade da e da bagade dawa: su dunu amo medole legemusa: sia: i) ema asili, ema gebewane sia: sa: i.
15 Ya tambayi mai tsaro na sarki, “Me ya sa sarki ya fitar da wannan doka haka da fushi?” Sai Ariyok ya yi wa Daniyel bayanin batun.
Da: niele da A: lioge ema amane adole ba: i, “Abuliga hina bagade da bagade dawa: su Ba: bilone sogega esasulubi, amo medole legema: ne sia: bela: ?” Amalalu, A:lioge da Da: nielema bai olelei.
16 Da jin haka sai Daniyel ya tafi wurin sarki ya nemi ƙarin lokaci, domin yă bayyana wa sarki mafarkin da kuma fassararsa.
Amola Da: niele da hedolodafa asili, hina bagadema e da bagade dawa: su dunu amo hedolo mae medole legema: ne sia: si. Bai e da hina bagadema ea simasi bai olelemusa: dawa: i. Amo sia: nababeba: le hina bagade da defea sia: i dagoi.
17 Sa’an nan Daniyel ya komo gida ya kuma sanar wa abokansa Hananiya, Mishayel da Azariya, batun nan duka.
Amalalu, Da: niele e da hi diasuga bu ogobele asi. Amalu ea sama dunu udiana amo Ha: nanaia, Misa: iele amola A: salaia, ilima amo liligi huluane olelei.
18 Ya roƙe su su roƙi jinƙan Allah na sama domin wannan mafarki, saboda kada a kashe shi da abokansa tare da sauran masu hikima na Babilon.
E da ilima amane sia: i, “Ninia da Gode Hebene ganodini esala Ema sia: ne gadomu da defea. E da ninima asigili fidima: ne sia: ne gadomu da defea. Amola dadi gagui ilia da nini amola eno bagade dawa: su dunu gilisili medole legesa: besa: le, Hina Gode da ninima Nebiuga: denese ea simasi bai, amo ninima olelema: ne ninia da Ema adole ba: mu!” Da: niele da amane sia: i.
19 A wannan dare sai aka bayyana wa Daniyel mafarkin cikin wahayi. Daniyel kuwa ya ɗaukaka Allah na sama.
Amalalu, amo gasi ganodini, amo simasi bai dawa: mu gogolei galu, Gode Hifawane amo simasi bai Da: nielema olelei dagoi. Amo hou ba: beba: le, Da: niele da Hebene Godema bagadewane nodoi.
20 Ya ce, “Yabo ya tabbata ga sunan Allah har abada abadin; hikima da iko nasa ne.
Amola Da: niele e da amane nodoi, “Gode da gasa bagade amola bagadedafa dawa: su. Eso huluane mae fisili Ema nodonanumu da defea.
21 Yana sāke lokuta, yana tuɓe sarakuna yana kuma naɗa waɗansu. Yana ba da hikima ga masu hikima kuma ilimi ga masu basira.
E da eso huluane eso amola gibu ouligilala. Ea sia: beba: le, hina bagade da hina hamoma: ne heda: sa amola Ea sia: beba: le ilia da bu dafasa. E fawane da osobo bagade dunu ilima bagade dawa: su iaha.
22 Yakan bayyana zurfafa da ɓoyayyun abubuwa; ya san abin da yake cikin dare, haske kuwa yana zaune tare da shi.
Liligi huluane wamolegei amo Ea da dawa: le olelesa. Liligi gasi ganodini wamo dialebe amo huludafa E ba: lala. Hisu da hadigidafa amoga sisiga: i dagoi ba: sa.
23 Na gode maka ina yabonka, Allah na kakannina. Kai ka san hikima da iko, ka sanar da ni abin da muka tambaye ka, ka kuma sanar da mu mafarkin sarki.”
Di da na aowalalia Godedafa. Amaiba: le na da Dima nodosa, amola Dia Dio gaguia gadosa. Bai Di da nama gasa amola bagade dawa: su iaha. Amola Di da na sia: ne gadoi amo nabi dagoi. Di da hina bagade ea simasi bai nama noga: le olelebeba: le, ninia da hina bagadema adole imunusa: dawa: ,” Da: niele da amane nodone sia: ne gadoi.
24 Sai Daniyel ya tafi wurin Ariyok, wanda sarki ya sa yă kashe masu hikiman Babilon, ya kuma ce masa, “Kada ka kashe masu hikiman Babilon ka kai ni wurin sarki, ni kuma zan fassara masa mafarkinsa.”
Amaiba: le, Da: niele da A: lioge (ema hina bagade da bagade dawa: su dunu medole lelegema: ne sia: i) ema amane sia: i, “Amo dunu mae medole legema. Dia na hina bagade ema oule masa. Amalalu, na da ea simasia ba: i amo hima bai olelemu.”
25 Sai Ariyok ya kai Daniyel wurin sarki nan take ya ce masa, “Na gano wani mutum daga cikin kamammun kabilar Yahuda wanda zai faɗa wa sarki abin da mafarkin yake nufi.”
Amanoba, A:lioge da hedolodafa Da: niele amo hina bagadema oule asi. A: lioge da hina bagadema amane sia: i, “Na da Yuda mugululi asi dunu afae dima oule misi. Amo dunu da dia simasi bai amo olelemusa: dawa: !”
26 Sarki ya tambayi Daniyel (wanda ake kira Belteshazar), za ka iya faɗa mini mafarkin da na yi ka kuma fassara shi?
Hina bagade da Da: niele (ea dio eno da Beledesia: sa) ema amane adole ba: i, “Beledesia: sa! Di da na simasia ba: i ea hou amola ea bai amo nama olelemusa: dawa: bela: ?”
27 Daniyel ya amsa, “Babu wani mai hikima, ko mai sihiri, ko mai dabo ko mai duban da zai iya warware wa sarki wannan matsala da ta dame shi,
Da: niele da ema bu amane adole i, “Hina bagade! Dia simasia ba: i amo bai dima olelemusa: , ba: la: lusu o nabi dunu o wamuni dawa: su dunu da hamedafa esala.
28 amma akwai Allahn da yake a sama wanda yake bayyana asirai, ya nuna wa sarki Nebukadnezzar abin da zai faru a kwanaki masu zuwa. Mafarkinka da wahayin da ya wuce cikin tunaninka a sa’ad da kake kwance a gadonka su ne,
Be Godedafa da Hebene ganodini esala. Hifawane da wamolegei liligi huluane ba: musa: dawa: Gode da amo simasi ganodini hou fa: no misunu, amo liligi dima olelei dagoi. Wali na da amo simasi di da golaia ba: i, amo ea bai dima olelemu!”
29 “A sa’ad da kake kwance, ya sarki, tunaninka ya ga al’amuran da suke zuwa, kuma shi mai bayyana al’amuran ya bayyana maka asiran abubuwan da za su faru.
“Hina bagade! Di da golaia ba: i amo da Gode da fa: no misunu hou amo dima olelei. Amola Gode da wamolegei liligi huluane dawa: beba: le, E da fa: no misunu hou olelei dagoi.
30 Amma ba a bayyana mini wannan asiri saboda ina da wata hikima fiye da sauran mutane ba, sai dai domin a sanar wa sarki da fassarar, ka kuma san tunanin da ya shiga zuciyarka.
Gode da amo wamolegei liligi, nama olelei dagoi. Bai na da baligili bagade dawa: su dunu amo hame. Be bai Gode da di amo simasi ea bai amola dia asigi dawa: su ea bai noga: le dawa: mu, Gode da hanai galebe.
31 “Ya sarki, ka ga wata babbar siffa, mai girma, siffa ce mai haske, abar bantsoro tana tsaye a gabanka.
Hina bagade! Dia simasi amo ganodini di da dia midadi dununa hamoi bagadedafa babagala: lebe ba: i. Di da amo liligi ba: beba: le, bagade beda: i.
32 An yi kan wannan siffa da zinariya zalla, ƙirjinta da kuma hannuwanta an yi su da azurfa, cikinta da kuma cinyarta da tagulla ne.
Amo dununa hamoi bagadedafa ea busa: gi da gouliga hamoi. Ea bidegi amola ea lobo da silifa amoga hamoi. Amola ea bulu ga: su amola masele da balase amoga hamoi.
33 An yi ƙafafun da ƙarfe, tafin ƙafafunta kuma an yi rabi da ƙarfe rabi kuma da yumɓu.
Ea emo aduna amo da gasa bagade ouli amoga hamoi. Amola emo osa: su da ouli amola laga osobo amo gilisili amoga hamoi.
34 A lokacin da kake dubawa, sai aka yanko wani dutse, amma ba da hannun mutum ba. Ya fāɗa a kan ƙafafun siffar na ƙarfen da aka haɗa da yumɓu aka kuma ragargaje su.
Di amo dununa hamoi bagadedafa sosodolaloba, igi bagadedafa afae goumi da: iya ganodini agele dalebe ba: i. Amola amo igi da bebesola misini, amo dununa hamoi amo ea emo osa: su, (ouli amola laga osobo gilisili amoga hamoi), amo fai. Fabeba: le, ea emo da gagoudane fofonoboi.
35 Sai ƙarfen da yambun da tagulla da azurfan da kuma zinariyan suka ragargaje a lokaci ɗaya ya zama kamar ƙaiƙayi a masussuka a lokacin kaka. Sai iska ta kwashe su ta tafi, har ba a iya ganin ko alamarsu. Amma dutsen da ya fāɗo a siffar ya girke ya zama tsauni ya kuma cika dukan duniya.
Amalalu, hedolodafa, dununa hamoi liligi amo ouli, laga osobo, balase, silifa amola gouli amoga hamoi, amo liligi huluane goudane gulu agoai ba: i. Amola fo misini, amo gulu liligi amo huluane mini asili hamedafa ba: i. Be igi bagade amo da dununa hamoi liligi fai, amo da bagade alelalu, goumi bagade agoane ba: i. Amola amo goumi da osobo bagade huluane dedeboi dagoi.”
36 “Wannan shi ne mafarkin, yanzu kuma za mu fassara ta wa sarki.
Da: niele da hina bagadema amane sia: i, “Goe da dia simasi hou. Defea na da amo bai dima olelemu!”
37 Ya, sarki, kai ne sarkin sarakuna. Allah na sama ya ba ka iko da girma da suna;
“Hina bagade! Di da bisilua, hina bagade oda huluane baligi dagoi. Gode da Hebene diasuga esala, amola Hi fawane da di hina bagade hamoi. Hi hamobeba: le, di da gasa bagade lela amola dunu huluane ilia dia dio gaguia gadosa.
38 a cikin hannunka ya sanya ɗan adam, da namun jeji da tsuntsayen sama. A duk inda suke zaune, ya maishe ka ka yi mulki a bisansu kai ne kan zinariyan nan na siffar.
E da di, fifi asi gala dunu amola uda huluane amola ohe fi amola sio fi ilima hina bagade hamoi dagoi. Dia simasia ba: i amo ganodini dununa hamoi liligi amo ea busa: gi ba: i, amo da di fawane.
39 “A bayanka, za a yi wani mulki, wanda bai kai naka ba. A gaba kuma, za a yi mulki na uku wanda yake na tagulla, zai yi mulkin dukan duniya.
Be dia ouligisu hou da dagolalu, hina bagade eno da dia sogebi lamu. Ea fi da gasa bagade ba: mu be amo dunu ilia da dia gasa agoai hame ganumu. Amola bu fa: no da hina bagade eno da misini, ea da osobo bagade huluane ouligimu. Goe hina bagade da balase agoane, gasa bagade ba: mu.
40 A ƙarshe, za a yi mulki na huɗu, mai ƙarfi kamar ƙarfe, Da yake baƙin ƙarfe yakan kakkarya, ya ragargaje abubuwa, haka nan wannan mulki zai ragargaje sauran mulkoki
Fa: no da hina bagade biyadu misunu. Ea fi da gasa bagadeba: le, ilia da ouli agoai, liligi huluane fananu amo liligi da gagoudana ahoa. Amomane, ouli da liligi huluane gagoudasa, amo defele amo fi da musa: fi huluane goudane wadela: lesimu.
41 Ka kuma ga an yi ƙafafun da yatsotsin da baƙin ƙarfe gauraye da yumɓu, wato, mulkin zai rabu, amma zai kasance da ƙarfi kamar na baƙin ƙarfe da yake gauraye da yumɓu.
Amola dia simasia ba: i ea bai eno da agoane. Dununa hamoi ea emo osa: su amola emo sasafo da laga osobo amola ouli amoga gilisili hamoi. Amo bai da agoane. Fi misunu da afafae fi agoane ba: mu. Ouli da laga osobo amoma gilisibiba: le, ilia da fonobahadi ouli ea gasa defele ba: mu.
42 Kamar yadda yatsotsin rabi na ƙarfe rabi kuma na yumɓu ne, haka wannan mulki zai zama rabi mai ƙarfi rabi kuma marar ƙarfi.
Be emo sasafo da ouli amola laga osobo amoga gilisili hamoi, amo ea dawa: loma: ne da amo fi la: idi afae da gasa bagade ba: mu be la: idi eno da gasa hame ba: mu.
43 Kamar dai yadda ka ga ƙarfen ya gauraye da yumɓu, haka mutanen za su zama a gauraye amma ba za su haɗu da juna ba, kamar yadda baƙin ƙarfe da yumɓu ba su haɗuwa.
Amola ouli amola laga osobo da gilisi, amo di da ba: i dagoi. Amo bai da agoane. Amo fi dunu ilia hina bagade ilia da uda lasu hou amoga ilia sosogo fi huluane gilisili madelagimusa: dawa: mu. Be ouli amola laga osobo amo gilisili madelagimu da hamedei. Amo defele, amo fi ea sosogo fi gilisili madelagimu da hamedeiwane ba: mu.
44 “A lokacin mulkin waɗannan sarakunan, Allah na sama zai kafa mulki da ba zai taɓa rushewa ba, ba kuma za a ba ma waɗansu mutane ba. Zai ragargaje waɗannan mulkokin da kuma kawo su ga ƙarshe, amma shi wannan mulki zai dawwama har abada.
Amola goe hina bagade dunu esasulubi eso amoga Hebene esalebe Gode da Hinadafa Hou amo da eso huluane dialoma: ne hahamomu. Eno fi amola eno hou da amo Hinadafa Hou amo hasalasimu hamedeiwane ba: mu. Be Gode Ea Hinadafa Hou da amo gasa bagade fi huluane amo wadela: lesilalu, eso huluane dialumu.
45 Wannan shi ne ma’anar wannan wahayin da ka gani na dutsen da aka yanko daga jikin tsaunin, amma ba da hannun ɗan adam ba, dutsen da ya ragargaza ƙarfen, da tagullar, da yumɓun da azurfar da kuma zinariyar. “Allah mai girma ya nuna wa sarki abin da zai faru nan gaba. Mafarkin gaskiya ne, fassararsa kuma abin dogara ne.”
Di sosodolaloba, goumi gadodili igi agele dalebe ba: i. Amo igi enoga hame digili ba: iwane da sa: ili dununa hamoi amo ouli, balase, laga osobo, silifa amola gouli amoga hamoi, amo fai dagoi. Amola Gode Ea Dio da gadodafa, amo hou fa: no misunu hou dima olelei dagoi. Amola liligi huluane dia simasi ganodini sodoi amo bai huluane, na dima molole olelei dagoi!”
46 Sai sarki Nebukadnezzar ya fāɗi da fuskarsa har ƙasa a gaban Daniyel domin ya girmama shi ya kuma umarta a miƙa hadaya da kuma hadayar ƙonawa ta turare ga Daniyel.
Nebiuga: denese da Da: niele ea sia: i nababeba: le, e da osoboga begudui, amola ea fidisu dunuma ilia da Da: nielema nodonomusa: hahawane iasu amola gobele salasu hamoma: ne sia: i.
47 Sarki ya kuma ce wa Daniyel, “Tabbatacce Allahnka shi ne Allahn alloli da kuma Sarkin sarakuna da mai bayyana asirai, gama ka iya bayyana wannan asiri.”
Amalalu hina bagade da Da: nielema amane sia: i, “Dia Gode da ‘gode’ huluane baligi dagoi. E da hina bagade eno huluane baligisa. E da liligi wamolegei huludafa bai olelemusa: dawa: Na da wali amo hou dawa: i dagoi. Bai di da Gode ea gasaga amo wamolegei liligi nama olelei dagoi.
48 Sai sarki ya ɗora Daniyel a babban matsayi ya kuma sanya shi mai mulki a kan dukan yankin ƙasar Babilon; ya kuma ɗora shi yă zama mai kula da duk masu hikima.
Nebiuga: denese da Da: niele amo Ba: bilone sogega ouligisu dunu bagade hamoi dagoi. E da ema liligi noga: idafa bagohame udigili i. Amola Da: niele da ea fada: i sia: ne iasu dunu ilima hina esaloma: ne sia: i.
49 Bugu da ƙari, bisa ga bukatar Daniyel sai sarki yă naɗa Shadrak da Meshak da Abednego su zama masu kula da harkokin lardin Babilon, amma Daniyel kuma ya tsaya a fadar sarki.
Amola Da: niele da Nebiuga: denesema adole ba: beba: le, e da Sia: dala: ge, Misia: ge amola Abedenigou ilima Ba: bilone soge ganodini eagene hawa: hamosu i. Be Da: niele hifawane da hina bagade ea diasu ganodini esalumu sia: i dagoi.

< Daniyel 2 >