< Daniyel 12 >

1 “A wannan lokaci Mika’ilu, babban mai mulki wanda yake kāre mutanenka, zai tashi. Za a yi lokacin matsananciyar wahala wanda ba a taɓa yi tun farkon ƙasashe har zuwa yanzu. Amma a lokacin da mutanenka, kowane mutum wanda aka sami sunansa a rubuce a cikin littafin, za a cece shi.
آن فرستادهٔ آسمانی که لباس کتان بر تن داشت، در ادامهٔ سخنانش گفت: «در آن زمان، فرشتهٔ اعظم، میکائیل، به حمایت از قوم تو برخواهد خاست. سپس چنان دوران سختی پیش خواهد آمد که در تاریخ بشر بی‌سابقه بوده است، اما هر که از قوم تو نامش در کتاب خدا نوشته شده باشد، رستگار خواهد شد.
2 Ɗumbun mutanen da suka yi barci cikin turɓayar duniya za su farka, waɗansu zuwa ga rai madawwami, waɗansu zuwa ga madawwamiyar kunya da kuma madawwamin ƙasƙanci.
«تمام مردگان زنده خواهند شد بعضی برای زندگی جاودانی و برخی برای شرمساری و خواری جاودانی.
3 Waɗanda suke da hikima za su haskaka kamar hasken samaniya, waɗanda kuma suka jagoranci waɗansu da yawa zuwa adalci, za su zama kamar taurari har abada abadin.
«حکیمان همچون آفتاب خواهند درخشید و کسانی که بسیاری را به راه راست هدایت کرده‌اند، چون ستارگان تا ابد درخشان خواهند بود.»
4 Amma kai, Daniyel, ka rufe zancen nan ka kuma liƙe kalmomin littafin nan har sai ƙarshe. Mutane da yawa za su yi ta kai komo don neman sani.”
سپس به من گفت: «اما تو ای دانیال، این پیشگویی را مثل یک راز نگه دار؛ آن را مهر کن تا وقتی که زمان آخر فرا رسد. بسیاری به سرعت حرکت خواهند کرد و عِلم خواهد افزود.»
5 Sa’an nan ni, Daniyel, na duba, a gabana kuwa ga waɗansu mutum biyu tsaye, ɗaya a wannan hayen kogi ɗaya kuma a ƙetaren kogin.
آنگاه من، دانیال، نگاه کردم و دو نفر دیگر را نیز دیدم که یکی در این سوی رودخانه و دیگری در آن سوی آن ایستاده بودند.
6 Ɗayansu ya ce wa mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, “Har yaushe waɗannan abubuwan banmamakin za su cika?”
یکی از آنها از آن فرستادهٔ آسمانی که لباس کتان بر تن داشت و در این هنگام بالای رودخانه ایستاده بود، پرسید: «چقدر طول خواهد کشید تا این وقایع عجیب به پایان برسد؟»
7 Mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, ya ɗaga hannun damansa da kuma na hagunsa sama, sai na ji yana rantsuwa da wannan da yake raye har abada, yana cewa, “Zai kasance na ɗan lokaci, lokuta da rabin lokaci. Za a kammala waɗannan abubuwa, sa’ad da aka gama ragargaje ikon tsarkakan mutane.”
او در جواب، دو دست خود را به سوی آسمان بلند کرد و به خدایی که تا ابد باقی است قسم خورد و گفت: «این وضع تا سه سال و نیم طول خواهد کشید. وقتی ظلم و ستمی که بر قوم خدا می‌شود پایان یابد، این وقایع نیز به پایان خواهد رسید.»
8 Na kuma ji, amma ban fahimta ba. Don haka sai na yi tambaya, “Ranka yă daɗe, mene ne ƙarshen waɗannan abubuwa?”
آنچه را که او گفت شنیدم، ولی آن را درک نکردم. پس گفتم: «ای سرورم، آخر این وقایع چه خواهد شد.»
9 Sai ya amsa ya ce, “Ka kama hanyarka, Daniyel, domin a rufe kalmomin aka kuma liƙe su har sai ƙarshen lokaci.
او جواب داد: «ای دانیال، تو راه خود را ادامه بده، زیرا آنچه گفته‌ام مهر خواهد شد و مخفی خواهد ماند تا زمان آخر فرا رسد.
10 Za a tsarkake mutane da yawa, za a maishe su marasa aibi a kuma tace su; amma mugaye za su ci gaba da mugunta. Babu wani mugun da zai fahimta, amma waɗanda za su zama masu hikima za su fahimta.
عدهٔ زیادی پاک و طاهر خواهند شد، ولی بدکاران به کارهای بدشان ادامه خواهند داد. از بدکاران هیچ‌کدام چیزی نخواهند فهمید، اما حکیمان همه چیز را درک خواهند کرد.
11 “Daga lokacin da za a hana miƙa hadayar ƙonawa ta yau da kullum, a kuma kafa abin banƙyama, wanda yake lalatarwa, za a yi kwana 1,290.
«از وقتی که تقدیم قربانیهای روزانه منع شود و مکروه ویرانگر در خانهٔ خدا بر پا گردد، یک دورهٔ هزار و دویست و نود روزه سپری خواهد شد.
12 Mai albarka ne wanda ya jira har yă zuwa ƙarshen kwanakin nan 1,335.
خوشا به حال آن که صبر می‌کند تا به پایان دورهٔ هزار و سیصد و سی و پنج روزه برسد!
13 “Gare ka dai, ka yi tafiyarka har zuwa ƙarshe. Za ka huta, sa’an nan a ƙarshen kwanaki za ka tashi don karɓi sashen gadon da aka ba ka.”
«اما ای دانیال، تو راه خود را ادامه بده تا پایان زندگی‌ات فرا رسد و بیارامی. اما بدان که در زمان آخر زنده خواهی شد تا پاداش خود را بگیری.»

< Daniyel 12 >