< Daniyel 12 >

1 “A wannan lokaci Mika’ilu, babban mai mulki wanda yake kāre mutanenka, zai tashi. Za a yi lokacin matsananciyar wahala wanda ba a taɓa yi tun farkon ƙasashe har zuwa yanzu. Amma a lokacin da mutanenka, kowane mutum wanda aka sami sunansa a rubuce a cikin littafin, za a cece shi.
And at that time will Michael, the great prince who standeth for the children of thy people, stand forth; and there will be a time of distress, such as hath never been since the existence of any nation, until that same time; and at that time shall thy people be delivered, every one that shall be found written in the book.
2 Ɗumbun mutanen da suka yi barci cikin turɓayar duniya za su farka, waɗansu zuwa ga rai madawwami, waɗansu zuwa ga madawwamiyar kunya da kuma madawwamin ƙasƙanci.
And many of those that sleep in the dust of the earth shall awake, some to everlasting life, and some to disgrace and everlasting abhorrence.
3 Waɗanda suke da hikima za su haskaka kamar hasken samaniya, waɗanda kuma suka jagoranci waɗansu da yawa zuwa adalci, za su zama kamar taurari har abada abadin.
And the intelligent shall shine brilliantly like the brilliance of the expanse [of the sky]; and they that bring many to righteousness shall be like the stars, for ever and ever.
4 Amma kai, Daniyel, ka rufe zancen nan ka kuma liƙe kalmomin littafin nan har sai ƙarshe. Mutane da yawa za su yi ta kai komo don neman sani.”
But thou, O Daniel, close up the words, and seal the book, until the time of the end: many will roam about, yet shall knowledge be increased.
5 Sa’an nan ni, Daniyel, na duba, a gabana kuwa ga waɗansu mutum biyu tsaye, ɗaya a wannan hayen kogi ɗaya kuma a ƙetaren kogin.
Then I Daniel looked, and behold, there were two others standing, the one on this side of the bank of the stream, and the other on that side of the bank of the stream.
6 Ɗayansu ya ce wa mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, “Har yaushe waɗannan abubuwan banmamakin za su cika?”
And one said to the man clothed in linen, who was above the waters of the stream, How long shall it be to the end of these wonders?
7 Mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, ya ɗaga hannun damansa da kuma na hagunsa sama, sai na ji yana rantsuwa da wannan da yake raye har abada, yana cewa, “Zai kasance na ɗan lokaci, lokuta da rabin lokaci. Za a kammala waɗannan abubuwa, sa’ad da aka gama ragargaje ikon tsarkakan mutane.”
Then heard I the man clothed in linen, who was above the waters of the stream; and he lifted up his right hand and his left hand unto the heavens, and swore by the Everliving One that after a time, times, and a half, and when there shall be an end to the crushing of the power of the holy people, all these things shall be ended.
8 Na kuma ji, amma ban fahimta ba. Don haka sai na yi tambaya, “Ranka yă daɗe, mene ne ƙarshen waɗannan abubuwa?”
And I heard indeed, but I understood it not: then said I, O my lord, what shall be the end of these things?
9 Sai ya amsa ya ce, “Ka kama hanyarka, Daniyel, domin a rufe kalmomin aka kuma liƙe su har sai ƙarshen lokaci.
And he said, Go [thy way], Daniel; for the words are closed up and sealed till the time of the end.
10 Za a tsarkake mutane da yawa, za a maishe su marasa aibi a kuma tace su; amma mugaye za su ci gaba da mugunta. Babu wani mugun da zai fahimta, amma waɗanda za su zama masu hikima za su fahimta.
Many shall be selected and cleansed, and purified; but the wicked will deal wickedly, and none of the wicked will understand: but the intelligent will understand.
11 “Daga lokacin da za a hana miƙa hadayar ƙonawa ta yau da kullum, a kuma kafa abin banƙyama, wanda yake lalatarwa, za a yi kwana 1,290.
And from the time that the continual sacrifice will be removed, even to set up the desolating abomination, there will be a thousand two hundred and ninety days.
12 Mai albarka ne wanda ya jira har yă zuwa ƙarshen kwanakin nan 1,335.
Happy is he that waiteth, and attaineth to the thousand three hundred and five and thirty days.
13 “Gare ka dai, ka yi tafiyarka har zuwa ƙarshe. Za ka huta, sa’an nan a ƙarshen kwanaki za ka tashi don karɓi sashen gadon da aka ba ka.”
But thou, go [thy way] toward the end; and thou shalt rest, and arise again for thy lot at the end of the days.

< Daniyel 12 >