< Daniyel 12 >
1 “A wannan lokaci Mika’ilu, babban mai mulki wanda yake kāre mutanenka, zai tashi. Za a yi lokacin matsananciyar wahala wanda ba a taɓa yi tun farkon ƙasashe har zuwa yanzu. Amma a lokacin da mutanenka, kowane mutum wanda aka sami sunansa a rubuce a cikin littafin, za a cece shi.
But at that time shall Michael rise up, the great prince, who standeth for the children of thy people: and a time shall come such as never was from the time that nations began even until that time. And at that time shall thy people be saved, every one that shall be found written in the book.
2 Ɗumbun mutanen da suka yi barci cikin turɓayar duniya za su farka, waɗansu zuwa ga rai madawwami, waɗansu zuwa ga madawwamiyar kunya da kuma madawwamin ƙasƙanci.
And many of those that sleep in the dust of the earth, shall awake: some unto life everlasting, and others unto reproach, to see it always.
3 Waɗanda suke da hikima za su haskaka kamar hasken samaniya, waɗanda kuma suka jagoranci waɗansu da yawa zuwa adalci, za su zama kamar taurari har abada abadin.
But they that are learned shall shine as the brightness of the firmament: and they that instruct many to justice, as stars for all eternity.
4 Amma kai, Daniyel, ka rufe zancen nan ka kuma liƙe kalmomin littafin nan har sai ƙarshe. Mutane da yawa za su yi ta kai komo don neman sani.”
But thou, O Daniel, shut up the words, and seal the book, even to the time appointed: many shall pass over, and knowledge shall be manifold.
5 Sa’an nan ni, Daniyel, na duba, a gabana kuwa ga waɗansu mutum biyu tsaye, ɗaya a wannan hayen kogi ɗaya kuma a ƙetaren kogin.
And I Daniel looked, and behold as it were two others stood: one on this side upon the bank of the river, and another on that side, on the other bank of the river.
6 Ɗayansu ya ce wa mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, “Har yaushe waɗannan abubuwan banmamakin za su cika?”
And I said to the man that was clothed In linen, that stood upon the waters of the river: How long shall it be to the end of these wonders?
7 Mutumin da yake sanye da tufafin lilin, wanda yake a saman ruwan kogin, ya ɗaga hannun damansa da kuma na hagunsa sama, sai na ji yana rantsuwa da wannan da yake raye har abada, yana cewa, “Zai kasance na ɗan lokaci, lokuta da rabin lokaci. Za a kammala waɗannan abubuwa, sa’ad da aka gama ragargaje ikon tsarkakan mutane.”
And I heard the man that was clothed in linen, that stood upon the waters of the river: when he had lifted up his right hand, and his left hand to heaven, and had sworn, by him that liveth for ever, that it should be unto a time, and times, and half a time. And when the scattering of the band of the holy people shall be accomplished, all these things shall be finished.
8 Na kuma ji, amma ban fahimta ba. Don haka sai na yi tambaya, “Ranka yă daɗe, mene ne ƙarshen waɗannan abubuwa?”
And I heard, and understood not. And I said: O my lord, what shall be after these things?
9 Sai ya amsa ya ce, “Ka kama hanyarka, Daniyel, domin a rufe kalmomin aka kuma liƙe su har sai ƙarshen lokaci.
And he said: Go, Daniel, because the words are shut up, and sealed until the appointed time.
10 Za a tsarkake mutane da yawa, za a maishe su marasa aibi a kuma tace su; amma mugaye za su ci gaba da mugunta. Babu wani mugun da zai fahimta, amma waɗanda za su zama masu hikima za su fahimta.
Many shall be chosen, and made white, and shall be tried as fire: and the wicked shall deal wickedly, and none of the wicked shall understand, but the learned shall understand.
11 “Daga lokacin da za a hana miƙa hadayar ƙonawa ta yau da kullum, a kuma kafa abin banƙyama, wanda yake lalatarwa, za a yi kwana 1,290.
And from the time when the continual sacrifice shall be taken away, and the abomination unto desolation shall be set up, there shall be a thousand two hundred ninety days,
12 Mai albarka ne wanda ya jira har yă zuwa ƙarshen kwanakin nan 1,335.
Blessed is he that waiteth and cometh unto a thousand three hundred thirty-five days.
13 “Gare ka dai, ka yi tafiyarka har zuwa ƙarshe. Za ka huta, sa’an nan a ƙarshen kwanaki za ka tashi don karɓi sashen gadon da aka ba ka.”
But go thou thy ways until the time appointed: and thou shalt rest, and stand in thy lot unto the end of the days.