< Daniyel 11 >
1 A shekara ta fari ta Dariyus mutumin Mede, na ɗauki matsayina domin in goyi baya in kuma kāre shi.)
I ja prve godine Darija Midijanina stadoh da mu pomožem, i da ga potkrijepim.
2 “Yanzu dai, zan faɗa maka gaskiya. Sarakuna uku za su taso a Farisa, sa’an nan kuma na huɗu, wanda zai fi dukansu dukiya. Sa’ad da zai sami iko saboda dukiyarsa, zai zuga dukan kowane mutum yă yi gāba da masarautar Girka.
A sada æu ti kazati istinu. Evo, još æe tri cara nastati u Persiji; i èetvrti æe biti bogatiji od svijeh, i kad se ukrijepi bogatstvom svojim, sve æe podignuti na Grèko carstvo.
3 Sa’an nan wani babban sarki zai bayyana, wanda zai yi mulki da babban iko yă kuma yi abin da ya ga dama.
Potom æe nastati silan car, i vladaæe velikom državom i radiæe što hoæe.
4 Bayan da ya bayyana, daularsa za tă wargaje za a rarraba ta zuwa kusurwoyi huɗu na duniya, a ba waɗansu waɗanda ba zuriyarsa ba, ba kuwa za su yi mulki da iko kamar yadda ya yi ba, gama za a tumɓuki daularsa a kuma ba wa waɗansu.
A kako nestane, rasuæe se carstvo njegovo i razdijeliæe se u èetiri vjetra nebeska, ne meðu natražje njegovo niti s vlašæu s kojom je on vladao, jer æe se carstvo njegovo ukinuti i dopasti drugima a ne njima.
5 “Sai sarki Kudu zai yi ƙarfi ƙwarai, amma ɗaya daga cikin komandodinsa zai yi ƙarfi fiye da shi, zai kuma yi mulki masarautarsa da iko mai girma.
I car južni osiliæe, i jedan od knezova njegovijeh, i biæe silniji od njega, i vladaæe, i država æe njegova biti velika.
6 Bayan’yan shekaru, za su haɗa kai. Diyar sarkin Kudu za tă je wurin sarkin Arewa ta sada zumunci, amma ba za tă riƙe iko ba, shi kuwa da ikonsa ba za su daɗe ba. A waɗannan kwanaki za a bashe ta, da ita da masu rakiyarta da kuma mahaifinta da kuma wanda ya goyi bayanta.
I poslije nekoliko godina oni æe se oprijateljiti, i kæi južnoga cara doæi æe k caru sjevernom da uèini pogodbu; ali ona neæe saèuvati sile mišici, niti æe se on održati s mišicom svojom, nego æe biti predana i ona i oni koji je dovedu i sin njezin i onaj koji joj bude pomagao u to vrijeme.
7 “Wani daga cikin zuriyarta zai taso yă ɗauki matsayinta. Zai kai wa sojojin sarkin Arewa hari yă kuma shiga kagararsa; zai yi yaƙi da su yă kuma yi nasara.
Potom æe od izdanka iz korijena njezina nastati jedan na mjesto njegovo, koji æe doæi s vojskom svojom i udariti na gradove cara sjevernoga, i biæe ih i osvojiæe ih.
8 Zai ƙwace allolinsu, siffofinsu na ƙarfe da kuma kaya masu daraja na azurfa da na zinariya a kuma kai su Masar. Zai yi’yan shekaru bai kai wa sarkin Arewa yaƙi ba.
I bogove æe njihove i knezove njihove sa zakladima njihovijem dragocjenijem zlatnijem i srebrnijem odnijeti u ropstvo u Misir, i ostaæe nekoliko godina jaèi od cara sjevernoga.
9 Sa’an nan sarkin Arewa zai kai wa sarkin Kudu hari, amma zai janye, yă koma ƙasarsa.
I tako æe car južni doæi u svoje carstvo, i vratiæe se u svoju zemlju.
10 ’Ya’yansa maza za su yi shirin yaƙi za su kuma tattara babbar rundunar sojoji, waɗanda za su yi ta mamayewa kamar rigyawar da ba iya tarewa, kuma za su kai yaƙin har kagararsa.
Ali æe sinovi njegovi zaratiti, i skupiæe veliku vojsku; i jedan æe doæi iznenada, i poplaviti i proæi; i vrativši se ratovaæe do grada njegova.
11 “Sa’an nan sai sarkin Kudu zai kama hanya da fushi zuwa yaƙi da sarkin Arewa, wanda zai tattara babbar rundunar yaƙi, amma za a ci shi da yaƙi.
Tada æe se razljutiti car južni, i izaæi æe i ratovaæe s njim, s carem sjevernijem, i podignuæe veliku vojsku, te æe mu biti data u ruke vojska.
12 Sa’ad da zai kawar da rundunar, sarkin Kudu zai cika da girman kai zai kuma kashe mutane dubbai, duk da haka ba zai kasance mai nasara ba.
I kad razbije vojsku, ponijeæe se srce njegovo, i pobiæe tisuæe, ali se neæe ukrijepiti.
13 Sarki Arewa kuma zai ƙara tara babbar rundunar soja, wadda ta fi ta dā girma; bayan waɗansu shekaru kuma, zai tafi yaƙi da babbar rundunar mayaƙa cike da kayan yaƙi.
Jer æe car sjeverni opet dignuti vojsku veæu od prve; i poslije nekoliko godina doæi æe s velikom vojskom i s velikim blagom.
14 “A waɗannan lokutan mutane da yawa za su tashi gāba da sarkin Kudu. Amma waɗansu’yan kama-karya za su taso daga jama’arka da niyya su cika abin da wahayin ya ce, amma za a fatattake su.
I u to æe vrijeme mnogi ustati na cara južnoga; i zlikovci od tvojega naroda podignuæe se da se potvrdi utvara, i popadaæe.
15 Sa’an nan sarkin arewa zai zo ya gina mahaurai a jikin katagar birni don yă ci birnin da yaƙi. Sojojin nan na Kudu kuwa ba za su iya tsayawa ba, ko zaɓaɓɓun jarumawansu ma, gama za su rasa ƙarfin tsayawa.
I doæi æe car sjeverni, i naèiniæe opkope, i uzeæe tvrde gradove, i mišice južnoga cara neæe odoljeti ni izabrani narod njegov, niti æe biti sile da se opre.
16 Wanda ya kai harin zai yi yadda ya ga dama, ba wanda zai iya ja da shi. Zai kafa kansa a Kyakkyawar Ƙasa zai kuma sami ikon da zai hallaka ta.
I onaj došav na nj èiniæe što hoæe, i neæe biti nikoga da mu se opre; i ustaviæe se u krasnoj zemlji, koju æe potrti svojom rukom.
17 Zai yunƙura yă zo da ƙarfin dukan masarautarsa zai kuma nemi haɗinkan sarkin Kudu. Zai kuma ba shi diyarsa yă aura don yă lalatar da mulkin, amma shirinsa ba zai yi nasara ba ko yă taimake shi ba.
Potom æe okrenuti da doðe sa silom svega carstva svojega, ali æe se pogoditi s njim, i daæe mu kæer za ženu da bi ga upropastio, ali se ona neæe držati, niti æe biti s njim.
18 Sa’an nan zai mai da hankalinsa zuwa ƙasashe a bakin kogi, zai kuma kama da yawansu, amma wani komanda zai kawo ƙarshen faɗin ransa, zai kuma sa faɗin ransa yă koma masa.
Potom æe se okrenuti na ostrva, i osvojiæe mnoga; ali æe jedan vojvoda prekinuti sramotu koju èini, i oboriæe na nj sramotu njegovu.
19 Bayan wannan, zai juya ga kagarar ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe yă fāɗi, ba kuwa za a ƙara ganinsa ba.
Potom æe se okrenuti ka gradovima svoje zemlje, i spotaknuæe se i pašæe, i neæe se više naæi.
20 “Magājinsa zai aiki mai karɓar haraji don darajar masarautarsa. Amma ba da daɗewa ba za a hallaka shi, duk da haka ba da fushi ko cikin yaƙi ba.
I na njegovo æe mjesto nastati koji æe poslati nastojnika u slavi carskoj; ali æe za malo dana poginuti bez gnjeva i bez boja.
21 “Magājin wannan sarki zai zama wani mutumin banza wanda ma bai fito daga gidan sarauta ba. Zai taso ba zato ba tsammani, yă ƙwace sarautar ta hanyar zamba.
A na njegovo æe mjesto doæi neznatan èovjek, kome nije namijenjena èast carska; ali æe doæi mirno i osvojiæe carstvo laskanjem.
22 Sa’an nan zai shafe mayaƙa masu yawa a gabansa; zai hallaka har da waɗanda suke mulki na alkawari.
I mišice koje plave on æe poplaviti i polomiti, pa i kneza s kojim je uèinio vjeru.
23 Bayan ƙulla yarjejjeniya da shi, zai yi zamba cikin aminci, kuma zai sami damar hawan mulki da goyon baya mutane kaɗan.
Jer udruživši se s njim uèiniæe prijevaru, i došavši nadvladaæe s malo naroda.
24 Sa’ad da yankuna mafi arziki suke ji kome lafiya yake, zai kai musu hari kuma Zai aikata abin da kakanninsa ba su taɓa yi ba. Zai rarraba abin da aka kwaso daga yaƙi, da ganima, da dukiya ga dukan mabiyansa. Zai kuma yi shiri yă kai wa mafaka hari, amma na ɗan lokaci ne kawai.
I doæi æe mirno u rodna mjesta u zemlji, i uèiniæe što ni ocevi njegovi ni ocevi otaca njegovijeh ne uèiniše, razdijeliæe im plijen i grabež i blago, i smišljaæe misli na gradove, za neko vrijeme.
25 “Tare da babbar rundunar mayaƙa zai yi ƙarfin hali yă far wa sarkin Kudu da yaƙi. Sarkin kudu zai haɗa babbar rundunar soja mai ƙarfi don yaƙin, amma ba zai iya karo da shi ba, domin za a shirya masa maƙarƙashiya.
Potom æe podignuti silu svoju i srce svoje na cara južnoga s velikom vojskom; i car æe južni doæi u boj s velikom i vrlo silnom vojskom; ali neæe odoljeti, jer æe mu se èiniti nevjera.
26 Waɗanda suke ci daga tanadin sarki za su yi ƙoƙari su hallaka shi; za a share mayaƙansa, kuma za a kashe mutane masu yawa a yaƙin.
I koji jedu hljeb njegov satræe ga; vojska æe njegova poplaviti, i mnogi æe pasti pobijeni.
27 Sarakunan nan biyu sun sa mugunta a ransu. Za su zauna a tebur guda su yi ta shara wa juna ƙarya, amma a banza, gama lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna.
I srce æe obojice careva raditi o zlu, i za jednijem æe stolom lagati; ali se neæe izvršiti; jer æe kraj još biti u odreðeno vrijeme.
28 “Sarkin Arewa zai koma ƙasarsa da dukiya mai girma, amma zuciyarsa za tă yi gāba da tsattsarkan alkawari. Zai ɗauki mataki a kan wannan abu sa’an nan yă koma ƙasarsa.
I tako æe se vratiti u svoju zemlju s velikim blagom; i srce æe se njegovo obratiti na sveti zavjet, i kad izvrši, vratiæe se u svoju zemlju.
29 “A ƙayyadadden lokaci zai sāke kai wa Kudu hari, amma a wannan karo abin da zai faru zai sha bamban daga abin da ya faru can baya.
U odreðeno æe vrijeme opet doæi na jug; ali drugi put neæe biti kao prvi put.
30 Jiragen ruwa yammancin bakin teku za su yi gāba da shi, zuciyarsa kuwa za tă yi sanyi. Sa’an nan zai juya ya huce haushinsa a kan tsattsarkan alkawari. Zai komo yă nuna jinƙai ga waɗanda suka juya wa tsattsarkan alkawari baya.
Jer æe doæi na nj laðe Kitejske, i on æe se ojaditi, te æe se vratiti; i razljutiæe se na sveti zavjet, i izvršiæe; i vrativši se složiæe se s onima koji ostavljaju sveti zavjet.
31 “Mayaƙansa za su taso su ƙazantar da kagarar haikali za su kuma kawar da hadaya ta kullum. Sa’an nan za su kafa abin banƙyama da yake lalatarwa.
I vojska æe stajati uza nj, i oskvrniæe svetinju u gradu, i ukinuti žrtvu svagdašnju i postaviæe gnusobu pustošnu.
32 Ta wurin daɗin baki zai gurɓata waɗannan da suka karya alkawari, amma mutanen da suka san Allahnsu za su yi tsayin daka su yi jayayya da shi.
I koji su bezbožni prema zavjetu, on æe ih laskanjem otpaditi; ali narod koji poznaje Boga svojega ohrabriæe se i izvršiæe.
33 “Waɗanda suke da hikima za su wayar da kan mutane da yawa, duk da haka za a kashe su da takobi, waɗansu da wuta, a washe waɗansu a kai su bauta.
I razumni u narodu nauèiæe mnoge, i padaæe od maèa i ognja, ropstva i grabeža mnogo vremena.
34 Sa’ad da suka fāɗi, za su sami ɗan taimako, mutane da yawa za su haɗa kai da su, amma da munafunci.
Ali padajuæi dobiæe malu pomoæ; i mnogi æe pristati s njima dvolièeæi.
35 Waɗansu masu hikima za su yi tuntuɓe, don a tsabtacce su, a tsarkake su, su yi tsab, har matuƙar da aka ƙayyade ta yi.
I od razumnijeh æe pasti neki da bi se okušali i oèistili i ubijelili do roka, jer æe još biti rok.
36 “Sarkin zai yi abin da ya ga dama. Zai ɗaukaka yă kuma girmama kansa gaba da kowane allah zai kuma faɗa munanan abubuwa a kan Allahn alloli. Zai yi nasara har sai lokacin hukunci ya cika, gama abin da aka ƙaddara zai cika.
I taj æe car èiniti što hoæe, i podignuæe se i uzvisiæe se iznad svakoga boga, i èudno æe govoriti na Boga nad bogovima, i biæe sreæan dokle se ne svrši gnjev, jer æe se izvršiti što je odreðeno.
37 Ba zai kula da alloli iyayensa ba ko wanda mata suke sha’awa, balle ma yă ga darajar wani allah, amma zai ɗaukaka kansa gaba da su duka.
Neæe mariti ni za bogove svojih otaca ni za ljubav žensku, niti æe za koga boga mariti, nego æe se uzvišivati nada sve.
38 A maimakonsu, zai ɗaukaka allahn kagarai; allahn da kakanninsa ba su ko sani ba, shi ne zai miƙa masa zinariya, da azurfa, da duwatsu masu daraja, da abubuwa masu tsada.
I na mjesto Boga najsilnijega slaviæe boga kojega oci njegovi ne znaše, slaviæe zlatom i srebrom i dragim kamenjem i zakladima.
39 Zai kai wa kagarai mafi ƙarfi hari da taimakon baƙon allah zai kuma girmama waɗanda suka yarda da shi zai ba su girma, ya kuma shugabantar da su a kan mutane da yawa, zai raba musu ƙasa ta zama ladansu.
I uèiniæe da gradovi Boga najsilnijega budu boga tuðega; koje pozna umnožiæe im slavu i uèiniæe ih gospodarima nad mnogima i razdijeliæe zemlju mjesto plate.
40 “A lokaci ƙarshe sarkin Kudu zai tasar masa da yaƙi, sarkin Arewa kuwa zai tunzura, yă tasar masa da kekunan yaƙi da mahayan dawakai, da jiragen ruwa da yawa. Zai ratsa ƙasashe, yă ci su da yaƙi, yă wuce.
A u pošljednje vrijeme južni æe se car pobiti s njim; i car æe sjeverni udariti na nj kao vihor s kolima i konjicima i s mnogim laðama, i ušavši u zemlje poplaviæe i proæi.
41 Zai kuma mamaye Kyakkyawa Ƙasa. Ƙasashe masu yawa za su fāɗi, amma Edom, Mowab da kuma shugabannin Ammon za su kuɓuta daga hannunsa.
I doæi æe u krasnu zemlju, i mnogi æe propasti, a ove æe se izbaviti od njegovijeh ruku: Edomska, Moavska i glavni dio sinova Amonovijeh.
42 Zai fadada mulkinsa har zuwa ƙasashe masu yawa; Masar ma ba za tă tsira ba.
I posegnuæe rukom svojom na zemlje, i zemlja Misirska neæe umaknuti.
43 Zai mallaki dukiyoyi na zinariya, da na azurfa, da dukan abubuwa masu tsada na Masar. Zai kuma ci Libiyawa da Kush da yaƙi.
I osvojiæe blago u zlatu i u srebru i sve zaklade Misirske; i Livijani i Etiopljani iæi æe za njim.
44 Amma labari daga gabas da arewa za su firgita shi, shi kuwa zai ci gaba da yin yaƙi da zafi, yă karkashe mutane da yawa, yă shafe su.
Ali æe ga glasovi s istoka i sa sjevera smesti, te æe izaæi s velikim gnjevom da pogubi i zatre mnoge.
45 Zai kafa tentin mulkinsa tsakanin tekunan da suke a kyakkyawan tsauni mai tsarki. Duk da haka zai zo ga ƙarshensa, kuma babu wanda zai taimake shi.
I razapeæe šatore dvora svojega meðu morima na krasnoj svetoj gori; i kad doðe k svome kraju, niko mu neæe pomoæi.