< Daniyel 11 >

1 A shekara ta fari ta Dariyus mutumin Mede, na ɗauki matsayina domin in goyi baya in kuma kāre shi.)
Or moi, dès la première année de Darius le Mède, je me prêtais à ce qu’il devint fort et puissant.
2 “Yanzu dai, zan faɗa maka gaskiya. Sarakuna uku za su taso a Farisa, sa’an nan kuma na huɗu, wanda zai fi dukansu dukiya. Sa’ad da zai sami iko saboda dukiyarsa, zai zuga dukan kowane mutum yă yi gāba da masarautar Girka.
Et maintenant je vous annoncerai la vérité. Voici qu’il y aura encore trois rois en Perse, et le quatrième s’enrichira de très grandes richesses par-dessus tous les autres; et lorsqu’il sera devenu puissant par ses richesses, il animera tous les peuples contre le royaume de la Grèce.
3 Sa’an nan wani babban sarki zai bayyana, wanda zai yi mulki da babban iko yă kuma yi abin da ya ga dama.
Mais il s’élèvera un roi fort, et il dominera avec une grande puissance, et il fera ce qui lui plaira.
4 Bayan da ya bayyana, daularsa za tă wargaje za a rarraba ta zuwa kusurwoyi huɗu na duniya, a ba waɗansu waɗanda ba zuriyarsa ba, ba kuwa za su yi mulki da iko kamar yadda ya yi ba, gama za a tumɓuki daularsa a kuma ba wa waɗansu.
Et lorsqu’il sera affermi, son royaume sera brisé, et sera partagé vers les vents du ciel, mais non pas entre ses descendants, ni selon la puissance avec laquelle il aura dominé; car son royaume sera déchiré et passera à des étrangers outre ceux-là.
5 “Sai sarki Kudu zai yi ƙarfi ƙwarai, amma ɗaya daga cikin komandodinsa zai yi ƙarfi fiye da shi, zai kuma yi mulki masarautarsa da iko mai girma.
Et le roi du midi se fortifiera, et un de ses princes prévaudra sur lui, et il dominera par sa puissance, car grande sera sa domination.
6 Bayan’yan shekaru, za su haɗa kai. Diyar sarkin Kudu za tă je wurin sarkin Arewa ta sada zumunci, amma ba za tă riƙe iko ba, shi kuwa da ikonsa ba za su daɗe ba. A waɗannan kwanaki za a bashe ta, da ita da masu rakiyarta da kuma mahaifinta da kuma wanda ya goyi bayanta.
Et, après des années accomplies, ils feront alliance; et la fille du roi du midi viendra vers le roi de l’aquilon pour faire amitié; mais elle n’acquerra pas la force du bras, et sa race ne subsistera pas; et elle sera livrée, elle et les jeunes hommes qui l’ont amenée, et ceux qui la soutenaient en ces temps-là.
7 “Wani daga cikin zuriyarta zai taso yă ɗauki matsayinta. Zai kai wa sojojin sarkin Arewa hari yă kuma shiga kagararsa; zai yi yaƙi da su yă kuma yi nasara.
Et il s’élèvera du germe de ses racines un plant; et il viendra avec une armée, et entrera dans la province du roi de l’aquilon, et il les maltraitera, et il s’en rendra le maître.
8 Zai ƙwace allolinsu, siffofinsu na ƙarfe da kuma kaya masu daraja na azurfa da na zinariya a kuma kai su Masar. Zai yi’yan shekaru bai kai wa sarkin Arewa yaƙi ba.
Et de plus, il emmènera captifs en Egypte leurs dieux, et leurs images taillées au ciseau comme aussi les vases précieux d’argent et d’or; celui-là prévaudra contre le roi de l’aquilon.
9 Sa’an nan sarkin Arewa zai kai wa sarkin Kudu hari, amma zai janye, yă koma ƙasarsa.
Et le roi du midi entrera dans son royaume, puis il reviendra dans son propre pays.
10 ’Ya’yansa maza za su yi shirin yaƙi za su kuma tattara babbar rundunar sojoji, waɗanda za su yi ta mamayewa kamar rigyawar da ba iya tarewa, kuma za su kai yaƙin har kagararsa.
Mais ses fils seront irrités et assembleront une multitude de très nombreuses armées; et l’un deux viendra, se hâtant et se répandant partout; et il reviendra, et il s’animera, et il combattra contre ses forces.
11 “Sa’an nan sai sarkin Kudu zai kama hanya da fushi zuwa yaƙi da sarkin Arewa, wanda zai tattara babbar rundunar yaƙi, amma za a ci shi da yaƙi.
Et irrité, le roi du midi sortira et combattra contre le roi de l’aquilon; il préparera une très grande multitude de troupes, et une multitude sera livrée en sa main.
12 Sa’ad da zai kawar da rundunar, sarkin Kudu zai cika da girman kai zai kuma kashe mutane dubbai, duk da haka ba zai kasance mai nasara ba.
Et il prendra la multitude, et son cœur s’élèvera; et il abattra beaucoup de milliers; mais il ne prévaudra pas.
13 Sarki Arewa kuma zai ƙara tara babbar rundunar soja, wadda ta fi ta dā girma; bayan waɗansu shekaru kuma, zai tafi yaƙi da babbar rundunar mayaƙa cike da kayan yaƙi.
Car le roi de l’aquilon reviendra, et préparera une multitude beaucoup plus grande qu’auparavant; et à la fin des temps et des années, il viendra se hâtant avec une grande armée et des forces immenses.
14 “A waɗannan lokutan mutane da yawa za su tashi gāba da sarkin Kudu. Amma waɗansu’yan kama-karya za su taso daga jama’arka da niyya su cika abin da wahayin ya ce, amma za a fatattake su.
Et dans ces temps-là, un grand nombre s’élèveront contre le roi du midi; et aussi les fils des prévaricateurs de ton peuple s’élèveront, afin qu’ils accomplissent la vision, et ils tomberont.
15 Sa’an nan sarkin arewa zai zo ya gina mahaurai a jikin katagar birni don yă ci birnin da yaƙi. Sojojin nan na Kudu kuwa ba za su iya tsayawa ba, ko zaɓaɓɓun jarumawansu ma, gama za su rasa ƙarfin tsayawa.
Et le roi de l’aquilon viendra, et il formera un rempart, et il prendra des villes très fortifiées; et les bras du midi ne pourront soutenir l’attaque, et ses hommes d’élite s’élèveront pour résister, et ils n’auront pas de force.
16 Wanda ya kai harin zai yi yadda ya ga dama, ba wanda zai iya ja da shi. Zai kafa kansa a Kyakkyawar Ƙasa zai kuma sami ikon da zai hallaka ta.
Et venant sur lui, il fera selon qu’il lui plaira, et il n’y aura personne qui tienne devant sa face; et il s’arrêtera dans la terre illustre, et elle sera détruite par ses mains.
17 Zai yunƙura yă zo da ƙarfin dukan masarautarsa zai kuma nemi haɗinkan sarkin Kudu. Zai kuma ba shi diyarsa yă aura don yă lalatar da mulkin, amma shirinsa ba zai yi nasara ba ko yă taimake shi ba.
Et il posera sa face pour venir s’emparer de tout son royaume; il fera des conditions justes avec lui, il lui donnera une fille de ses femmes, afin de renverser son royaume; mais il ne réussira pas, et elle ne sera pas pour lui.
18 Sa’an nan zai mai da hankalinsa zuwa ƙasashe a bakin kogi, zai kuma kama da yawansu, amma wani komanda zai kawo ƙarshen faɗin ransa, zai kuma sa faɗin ransa yă koma masa.
Et il tournera sa face vers les îles, et il en prendra beaucoup; et il arrêtera le prince de son opprobre, et son opprobre retombera sur lui.
19 Bayan wannan, zai juya ga kagarar ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe yă fāɗi, ba kuwa za a ƙara ganinsa ba.
Et il tournera sa face vers la terre de son empire, et il se heurtera, et il tombera, et on ne le trouvera pas.
20 “Magājinsa zai aiki mai karɓar haraji don darajar masarautarsa. Amma ba da daɗewa ba za a hallaka shi, duk da haka ba da fushi ko cikin yaƙi ba.
Et il s’élèvera à sa place un homme très vil et indigne de la majesté royale; et en peu de jours il sera brisé, non dans la fureur ni dans un combat.
21 “Magājin wannan sarki zai zama wani mutumin banza wanda ma bai fito daga gidan sarauta ba. Zai taso ba zato ba tsammani, yă ƙwace sarautar ta hanyar zamba.
Et il s’élèvera à sa place un prince méprisé, et l’honneur royal ne lui sera pas rendu; et il viendra en secret, et il obtiendra le royaume par la fraude.
22 Sa’an nan zai shafe mayaƙa masu yawa a gabansa; zai hallaka har da waɗanda suke mulki na alkawari.
Et les bras du combattant seront vaincus devant sa face, et brisés, aussi bien que le chef de l’alliance.
23 Bayan ƙulla yarjejjeniya da shi, zai yi zamba cikin aminci, kuma zai sami damar hawan mulki da goyon baya mutane kaɗan.
Or, après l’amitié faite, il emploiera la fraude contre lui; et il montera, et il triomphera avec un peuple peu nombreux.
24 Sa’ad da yankuna mafi arziki suke ji kome lafiya yake, zai kai musu hari kuma Zai aikata abin da kakanninsa ba su taɓa yi ba. Zai rarraba abin da aka kwaso daga yaƙi, da ganima, da dukiya ga dukan mabiyansa. Zai kuma yi shiri yă kai wa mafaka hari, amma na ɗan lokaci ne kawai.
Et il entrera dans les villes riches et opulentes, et il fera ce que n’ont pas fait ses pères et les pères de ses pères: il dissipera leurs rapines, leur butin, leurs richesses, et il formera des desseins contre les villes les plus fortes; et cela jusqu’à un temps,
25 “Tare da babbar rundunar mayaƙa zai yi ƙarfin hali yă far wa sarkin Kudu da yaƙi. Sarkin kudu zai haɗa babbar rundunar soja mai ƙarfi don yaƙin, amma ba zai iya karo da shi ba, domin za a shirya masa maƙarƙashiya.
Et sa force et son cœur s’animeront contre le roi du midi, avec une grande armée; et le roi du midi sera excité au combat par des secours nombreux et très puissants; et ils ne résisteront pas, parce qu’il se formera contre lui des complots,
26 Waɗanda suke ci daga tanadin sarki za su yi ƙoƙari su hallaka shi; za a share mayaƙansa, kuma za a kashe mutane masu yawa a yaƙin.
Ceux qui mangent le pain avec lui le briseront; et son armée sera accablée, et il tombera une très grande quantité de tués,
27 Sarakunan nan biyu sun sa mugunta a ransu. Za su zauna a tebur guda su yi ta shara wa juna ƙarya, amma a banza, gama lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna.
Et le cœur des deux rois sera porté à mal faire; et à une même table ils parleront le mensonge; et ils ne réussiront pas, parce que la fin est pour un autre temps encore.
28 “Sarkin Arewa zai koma ƙasarsa da dukiya mai girma, amma zuciyarsa za tă yi gāba da tsattsarkan alkawari. Zai ɗauki mataki a kan wannan abu sa’an nan yă koma ƙasarsa.
Et il retournera dans son pays avec de grandes richesses; et son cœur sera contre l’alliance sainte; et il agira, et il retournera dans son pays.
29 “A ƙayyadadden lokaci zai sāke kai wa Kudu hari, amma a wannan karo abin da zai faru zai sha bamban daga abin da ya faru can baya.
Au temps marqué, il retournera, et il viendra vers le midi; mais sa dernière expédition ne sera pas semblable à la première.
30 Jiragen ruwa yammancin bakin teku za su yi gāba da shi, zuciyarsa kuwa za tă yi sanyi. Sa’an nan zai juya ya huce haushinsa a kan tsattsarkan alkawari. Zai komo yă nuna jinƙai ga waɗanda suka juya wa tsattsarkan alkawari baya.
Et viendront contre lui des trirèmes et des Romains; et il sera frappé, et il retournera, et il sera indigné contre l’alliance du sanctuaire, et il agira, et il retournera, et il formera des desseins même contre ceux qui ont abandonné l’alliance du sanctuaire.
31 “Mayaƙansa za su taso su ƙazantar da kagarar haikali za su kuma kawar da hadaya ta kullum. Sa’an nan za su kafa abin banƙyama da yake lalatarwa.
Et des bras armés par lui se lèveront, et souilleront le sanctuaire de la force, et feront cesser le sacrifice perpétuel, et ils ajouteront à l’abomination la désolation.
32 Ta wurin daɗin baki zai gurɓata waɗannan da suka karya alkawari, amma mutanen da suka san Allahnsu za su yi tsayin daka su yi jayayya da shi.
Et contre l’alliance, les impies useront d’une feinte trompeuse; mais le peuple connaissant son Dieu prévaudra et agira.
33 “Waɗanda suke da hikima za su wayar da kan mutane da yawa, duk da haka za a kashe su da takobi, waɗansu da wuta, a washe waɗansu a kai su bauta.
Et les savants parmi le peuple instruiront bien des gens, et ils tomberont sous le glaive, dans la flamme, en captivité, et par un brigandage de plusieurs jours.
34 Sa’ad da suka fāɗi, za su sami ɗan taimako, mutane da yawa za su haɗa kai da su, amma da munafunci.
Et lorsqu’ils seront tombés, ils seront soulagés par un très petit secours, et beaucoup se joindront à eux frauduleusement.
35 Waɗansu masu hikima za su yi tuntuɓe, don a tsabtacce su, a tsarkake su, su yi tsab, har matuƙar da aka ƙayyade ta yi.
Et d’entre ces savants, plusieurs succomberont, afin qu’ils passent par le feu, qu’ils soient purifiés, et qu’ils deviennent blancs jusqu’au temps déterminé, parce qu’il y aura encore un autre temps.
36 “Sarkin zai yi abin da ya ga dama. Zai ɗaukaka yă kuma girmama kansa gaba da kowane allah zai kuma faɗa munanan abubuwa a kan Allahn alloli. Zai yi nasara har sai lokacin hukunci ya cika, gama abin da aka ƙaddara zai cika.
Et le roi agira selon sa volonté, et il s’élèvera et se glorifiera, contre tout dieu; et contre le Dieu des dieux il parlera avec arrogance, et il prospérera, jusqu’à ce que le courroux de Dieu contre son peuple soit accompli; car la décision a été prise.
37 Ba zai kula da alloli iyayensa ba ko wanda mata suke sha’awa, balle ma yă ga darajar wani allah, amma zai ɗaukaka kansa gaba da su duka.
Et il comptera pour rien le Dieu de ses pères; et il sera livré à la concupiscence des femmes, et il n’aura souci d’aucun des dieux, parce qu’il s’élèvera contre toutes choses,
38 A maimakonsu, zai ɗaukaka allahn kagarai; allahn da kakanninsa ba su ko sani ba, shi ne zai miƙa masa zinariya, da azurfa, da duwatsu masu daraja, da abubuwa masu tsada.
Mais il vénérera en son lieu le dieu Maozim, et il honorera le dieu que ses pères ont ignoré, avec de l’or et de l’argent, et des pierres précieuses, et d’autres choses précieuses.
39 Zai kai wa kagarai mafi ƙarfi hari da taimakon baƙon allah zai kuma girmama waɗanda suka yarda da shi zai ba su girma, ya kuma shugabantar da su a kan mutane da yawa, zai raba musu ƙasa ta zama ladansu.
Et il fera en sorte de fortifier Maozim avec un dieu étranger qu’il a connu, et il multipliera leur gloire, et il leur donnera la puissance sur un grand nombre; et il partagera la terre gratuitement.
40 “A lokaci ƙarshe sarkin Kudu zai tasar masa da yaƙi, sarkin Arewa kuwa zai tunzura, yă tasar masa da kekunan yaƙi da mahayan dawakai, da jiragen ruwa da yawa. Zai ratsa ƙasashe, yă ci su da yaƙi, yă wuce.
Et, au temps marqué, le roi du midi combattra contre lui; et comme une tempête viendra contre lui le roi de l’aquilon, avec des chars et des cavaliers, et une grande flotte; et il entrera dans ses terres et les détruira, et passera au-delà.
41 Zai kuma mamaye Kyakkyawa Ƙasa. Ƙasashe masu yawa za su fāɗi, amma Edom, Mowab da kuma shugabannin Ammon za su kuɓuta daga hannunsa.
Et il entrera dans la terre glorieuse, et beaucoup de terres seront ruinées; or celles-là seules seront sauvées de sa main: Edom et Moab, et le commencement des fils d’Ammon.
42 Zai fadada mulkinsa har zuwa ƙasashe masu yawa; Masar ma ba za tă tsira ba.
Et il étendra sa main sur les terres, et la terre d’Egypte n’échappera pas.
43 Zai mallaki dukiyoyi na zinariya, da na azurfa, da dukan abubuwa masu tsada na Masar. Zai kuma ci Libiyawa da Kush da yaƙi.
Et il se rendra maître des trésors d’or et d’argent, et de toutes les choses précieuses de l’Egypte: il passera aussi au travers de la Libye et de l’Ethiopie.
44 Amma labari daga gabas da arewa za su firgita shi, shi kuwa zai ci gaba da yin yaƙi da zafi, yă karkashe mutane da yawa, yă shafe su.
Et des bruits venant de l’orient et de l’aquilon le troubleront; et il viendra avec une grande multitude, afin de briser et de tuer un très grand nombre.
45 Zai kafa tentin mulkinsa tsakanin tekunan da suke a kyakkyawan tsauni mai tsarki. Duk da haka zai zo ga ƙarshensa, kuma babu wanda zai taimake shi.
Et il plantera son tabernacle à Apadno entre des mers sur une montagne illustre et sainte; et il viendra jusqu’à son sommet, et personne ne le secourra.

< Daniyel 11 >