< Daniyel 11 >

1 A shekara ta fari ta Dariyus mutumin Mede, na ɗauki matsayina domin in goyi baya in kuma kāre shi.)
Or en la première année de Darius le Mède j'assistais pour l'affermir et le fortifier.
2 “Yanzu dai, zan faɗa maka gaskiya. Sarakuna uku za su taso a Farisa, sa’an nan kuma na huɗu, wanda zai fi dukansu dukiya. Sa’ad da zai sami iko saboda dukiyarsa, zai zuga dukan kowane mutum yă yi gāba da masarautar Girka.
Et maintenant aussi je te ferai savoir la vérité: Voici, il y aura encore trois Rois en Perse, puis le quatrième possédera de grandes richesses par-dessus tous; et s'étant fortifié par ses richesses il soulèvera tout [le monde] contre le Royaume de Javan.
3 Sa’an nan wani babban sarki zai bayyana, wanda zai yi mulki da babban iko yă kuma yi abin da ya ga dama.
Et un Roi puissant se lèvera, et dominera avec une grande puissance, et fera selon sa volonté.
4 Bayan da ya bayyana, daularsa za tă wargaje za a rarraba ta zuwa kusurwoyi huɗu na duniya, a ba waɗansu waɗanda ba zuriyarsa ba, ba kuwa za su yi mulki da iko kamar yadda ya yi ba, gama za a tumɓuki daularsa a kuma ba wa waɗansu.
Et sitôt qu'il sera en état, son Royaume sera brisé, et partagé vers les quatre vents des cieux, et ne sera point pour sa race, ni selon la domination avec laquelle il aura dominé: car son Royaume sera extirpé, et sera donné à d'autres, outre ceux-là.
5 “Sai sarki Kudu zai yi ƙarfi ƙwarai, amma ɗaya daga cikin komandodinsa zai yi ƙarfi fiye da shi, zai kuma yi mulki masarautarsa da iko mai girma.
Et le Roi du Midi sera fort puissant, mais un des principaux chefs du [Roi de Javan] sera plus puissant que [le Roi du Midi], et dominera, et sa domination [sera] une grande domination.
6 Bayan’yan shekaru, za su haɗa kai. Diyar sarkin Kudu za tă je wurin sarkin Arewa ta sada zumunci, amma ba za tă riƙe iko ba, shi kuwa da ikonsa ba za su daɗe ba. A waɗannan kwanaki za a bashe ta, da ita da masu rakiyarta da kuma mahaifinta da kuma wanda ya goyi bayanta.
Et au bout de [certaines] années ils s'allieront, et la fille du Roi du Midi viendra vers le Roi de l'Aquilon, pour redresser les affaires; mais elle ne retiendra point la force du bras, et [ni lui] ni son bras ne subsisteront point; mais elle sera livrée, et ceux aussi qui l'auront amenée, et celui qui sera né d'elle, et qui la fortifiait en ces temps-là.
7 “Wani daga cikin zuriyarta zai taso yă ɗauki matsayinta. Zai kai wa sojojin sarkin Arewa hari yă kuma shiga kagararsa; zai yi yaƙi da su yă kuma yi nasara.
Mais le soutien [du Royaume] du Midi s'élèvera d'un rejeton des racines d'elle, et viendra à l'armée, et entrera dans les forteresses du Roi de l'Aquilon, et y fera [de grands exploits], et se fortifiera.
8 Zai ƙwace allolinsu, siffofinsu na ƙarfe da kuma kaya masu daraja na azurfa da na zinariya a kuma kai su Masar. Zai yi’yan shekaru bai kai wa sarkin Arewa yaƙi ba.
Et même il emmènera captifs en Egypte leurs dieux avec les vaisseaux de leurs aspersions, et avec leurs vaisseaux précieux d'argent et d'or, et il subsistera quelques années plus que le Roi de l'Aquilon.
9 Sa’an nan sarkin Arewa zai kai wa sarkin Kudu hari, amma zai janye, yă koma ƙasarsa.
Et le Roi du Midi entrera dans [son] Royaume, mais il s'en retournera en son pays.
10 ’Ya’yansa maza za su yi shirin yaƙi za su kuma tattara babbar rundunar sojoji, waɗanda za su yi ta mamayewa kamar rigyawar da ba iya tarewa, kuma za su kai yaƙin har kagararsa.
Mais les fils de celui-là entreront en guerre, et assembleront une multitude de grandes armées; puis [l'un d'eux] viendra certainement, et se répandra, et passera; il retournera, dis-je, et s'avancera en bataille jusqu'à la forteresse [du Roi du Midi].
11 “Sa’an nan sai sarkin Kudu zai kama hanya da fushi zuwa yaƙi da sarkin Arewa, wanda zai tattara babbar rundunar yaƙi, amma za a ci shi da yaƙi.
Et le Roi du Midi sera irrité, et sortira, et combattra contre lui, [savoir] contre le Roi de l'Aquilon; et il assemblera une grande multitude, et cette multitude sera livrée entre les mains du Roi du Midi.
12 Sa’ad da zai kawar da rundunar, sarkin Kudu zai cika da girman kai zai kuma kashe mutane dubbai, duk da haka ba zai kasance mai nasara ba.
Et après avoir défait cette multitude il élèvera son cœur, et abattra des [gens] à milliers, mais il ne sera pas fortifié.
13 Sarki Arewa kuma zai ƙara tara babbar rundunar soja, wadda ta fi ta dā girma; bayan waɗansu shekaru kuma, zai tafi yaƙi da babbar rundunar mayaƙa cike da kayan yaƙi.
Car le Roi de l'Aquilon reviendra, et assemblera une plus grande multitude que la première, et au bout de quelque temps, [savoir], de quelques années, il viendra certainement avec une grande armée, et un grand appareil.
14 “A waɗannan lokutan mutane da yawa za su tashi gāba da sarkin Kudu. Amma waɗansu’yan kama-karya za su taso daga jama’arka da niyya su cika abin da wahayin ya ce, amma za a fatattake su.
Et en ce temps-là plusieurs s'élèveront contre le Roi du Midi; et les hommes violents de ton peuple s'élèveront, afin de confirmer la vision, mais ils tomberont.
15 Sa’an nan sarkin arewa zai zo ya gina mahaurai a jikin katagar birni don yă ci birnin da yaƙi. Sojojin nan na Kudu kuwa ba za su iya tsayawa ba, ko zaɓaɓɓun jarumawansu ma, gama za su rasa ƙarfin tsayawa.
Et le Roi de l'Aquilon viendra, et fera des terrasses, et prendra les villes fortes; et les bras du Midi, ni son peuple d'élite ne pourront point résister, car [il n'y aura] point de force pour résister.
16 Wanda ya kai harin zai yi yadda ya ga dama, ba wanda zai iya ja da shi. Zai kafa kansa a Kyakkyawar Ƙasa zai kuma sami ikon da zai hallaka ta.
Et il fera de celui qui sera venu contre lui, selon sa volonté, et il n'y aura personne qui tienne ferme devant lui; et il s'arrêtera au pays de noblesse, et il y aura consomption par sa force.
17 Zai yunƙura yă zo da ƙarfin dukan masarautarsa zai kuma nemi haɗinkan sarkin Kudu. Zai kuma ba shi diyarsa yă aura don yă lalatar da mulkin, amma shirinsa ba zai yi nasara ba ko yă taimake shi ba.
Puis il tournera sa face pour entrer par force dans tout le Royaume de celui-là, et ses affaires iront bien, et il fera de [grands exploits], et il lui donnera une fille de femmes, pour ruiner le Royaume; mais [cela] ne tiendra point, et elle ne sera point pour lui.
18 Sa’an nan zai mai da hankalinsa zuwa ƙasashe a bakin kogi, zai kuma kama da yawansu, amma wani komanda zai kawo ƙarshen faɗin ransa, zai kuma sa faɗin ransa yă koma masa.
Puis il tournera sa face vers les Iles, et en prendra plusieurs, mais un capitaine l'obligera de cesser l'opprobre qu'il faisait, et outre cela il fera retomber sur lui son opprobre.
19 Bayan wannan, zai juya ga kagarar ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe yă fāɗi, ba kuwa za a ƙara ganinsa ba.
Puis il tournera visage vers les forteresses de son pays, il heurtera, il sera renversé, et il ne sera plus trouvé.
20 “Magājinsa zai aiki mai karɓar haraji don darajar masarautarsa. Amma ba da daɗewa ba za a hallaka shi, duk da haka ba da fushi ko cikin yaƙi ba.
Et un autre sera établi en sa place, qui enverra l'exacteur pour la Majesté Royale, et il sera détruit dans peu de jours, mais non dans une rencontre, ni dans une bataille.
21 “Magājin wannan sarki zai zama wani mutumin banza wanda ma bai fito daga gidan sarauta ba. Zai taso ba zato ba tsammani, yă ƙwace sarautar ta hanyar zamba.
Et en sa place il en sera établi un autre qui sera méprisé, auquel on ne donnera point l'honneur royal; mais il viendra en paix, et il occupera le Royaume par des flatteries.
22 Sa’an nan zai shafe mayaƙa masu yawa a gabansa; zai hallaka har da waɗanda suke mulki na alkawari.
Et les bras des grandes eaux seront engloutis par un déluge devant lui, et seront rompus, et il sera le Chef d'un accord.
23 Bayan ƙulla yarjejjeniya da shi, zai yi zamba cikin aminci, kuma zai sami damar hawan mulki da goyon baya mutane kaɗan.
Mais après les accords faits avec lui, il usera de tromperie, et il montera, et se renforcera avec peu de gens.
24 Sa’ad da yankuna mafi arziki suke ji kome lafiya yake, zai kai musu hari kuma Zai aikata abin da kakanninsa ba su taɓa yi ba. Zai rarraba abin da aka kwaso daga yaƙi, da ganima, da dukiya ga dukan mabiyansa. Zai kuma yi shiri yă kai wa mafaka hari, amma na ɗan lokaci ne kawai.
Il entrera dans les lieux gras d'une Province [alors] paisible, et il fera des choses que ses pères, ni les pères de ses pères, n'ont point faites; il leur répandra le pillage, le butin, et les richesses; et il formera des desseins contre les forteresses: et cela jusqu'à un certain temps.
25 “Tare da babbar rundunar mayaƙa zai yi ƙarfin hali yă far wa sarkin Kudu da yaƙi. Sarkin kudu zai haɗa babbar rundunar soja mai ƙarfi don yaƙin, amma ba zai iya karo da shi ba, domin za a shirya masa maƙarƙashiya.
Puis il réveillera sa force et son cœur contre le Roi du Midi, avec une grande armée, et le Roi du Midi s'avancera en bataille avec une très grande et très forte armée, mais il ne subsistera point, parce qu'on formera des entreprises contre lui.
26 Waɗanda suke ci daga tanadin sarki za su yi ƙoƙari su hallaka shi; za a share mayaƙansa, kuma za a kashe mutane masu yawa a yaƙin.
Et ceux qui mangent les mets de sa table le mettront en pièces, et son armée sera accablée, comme d'un déluge, et beaucoup de gens tomberont blessés à mort.
27 Sarakunan nan biyu sun sa mugunta a ransu. Za su zauna a tebur guda su yi ta shara wa juna ƙarya, amma a banza, gama lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna.
Et le cœur de ces deux Rois sera [adonné] à s'entre-nuire, et ils parleront en une même table avec tromperie, ce qui ne tournera point à bien; car il y aura encore une fin au temps ordonné.
28 “Sarkin Arewa zai koma ƙasarsa da dukiya mai girma, amma zuciyarsa za tă yi gāba da tsattsarkan alkawari. Zai ɗauki mataki a kan wannan abu sa’an nan yă koma ƙasarsa.
Après quoi il s'en retournera en son pays avec de grandes richesses, et son cœur sera contre la sainte alliance, et il fera [de grands exploits], puis il retournera en son pays.
29 “A ƙayyadadden lokaci zai sāke kai wa Kudu hari, amma a wannan karo abin da zai faru zai sha bamban daga abin da ya faru can baya.
[Ensuite] il retournera au temps préfix, et il viendra contre le Midi, mais cette dernière [expédition] ne sera pas comme la précédente.
30 Jiragen ruwa yammancin bakin teku za su yi gāba da shi, zuciyarsa kuwa za tă yi sanyi. Sa’an nan zai juya ya huce haushinsa a kan tsattsarkan alkawari. Zai komo yă nuna jinƙai ga waɗanda suka juya wa tsattsarkan alkawari baya.
Car les navires de Kittim viendront contre lui, dont il sera contristé, et il s'en retournera, et il sera irrité contre la sainte alliance, et fera [de grands exploits], et retournera, et s'entendra avec les apostats de la sainte alliance.
31 “Mayaƙansa za su taso su ƙazantar da kagarar haikali za su kuma kawar da hadaya ta kullum. Sa’an nan za su kafa abin banƙyama da yake lalatarwa.
Et les forces seront de son côté, et on souillera le Sanctuaire, qui est la forteresse, et on ôtera le sacrifice continuel, et on y mettra l'abomination qui causera la désolation.
32 Ta wurin daɗin baki zai gurɓata waɗannan da suka karya alkawari, amma mutanen da suka san Allahnsu za su yi tsayin daka su yi jayayya da shi.
Et il fera pécher par flatteries ceux qui se porteront méchamment dans l'alliance; mais le peuple de ceux qui connaîtront leur Dieu se fortifiera, et fera [de grands exploits.]
33 “Waɗanda suke da hikima za su wayar da kan mutane da yawa, duk da haka za a kashe su da takobi, waɗansu da wuta, a washe waɗansu a kai su bauta.
Et les plus intelligents d'entre le peuple donneront instruction à plusieurs, et il y en aura qui tomberont par l'épée et par la flamme, ou qui seront en captivité et en proie durant plusieurs jours.
34 Sa’ad da suka fāɗi, za su sami ɗan taimako, mutane da yawa za su haɗa kai da su, amma da munafunci.
Et lorsqu'ils tomberont ainsi, ils seront un peu secourus; mais plusieurs se joindront à eux sous un beau semblant.
35 Waɗansu masu hikima za su yi tuntuɓe, don a tsabtacce su, a tsarkake su, su yi tsab, har matuƙar da aka ƙayyade ta yi.
Et quelques-uns de ces plus intelligents tomberont, afin qu'il y en ait d'entre eux qui soient rendus éprouvés, qui soient épurés, et qui soient blanchis, jusqu'au temps déterminé; car cela est encore pour un certain temps.
36 “Sarkin zai yi abin da ya ga dama. Zai ɗaukaka yă kuma girmama kansa gaba da kowane allah zai kuma faɗa munanan abubuwa a kan Allahn alloli. Zai yi nasara har sai lokacin hukunci ya cika, gama abin da aka ƙaddara zai cika.
Ce Roi donc fera selon sa volonté, et s'enorgueillira, et s'élèvera par-dessus tout Dieu; il proférera des choses étranges contre le Dieu des dieux, et prospérera jusqu'à ce que l'indignation ait pris fin; car la détermination en a été faite.
37 Ba zai kula da alloli iyayensa ba ko wanda mata suke sha’awa, balle ma yă ga darajar wani allah, amma zai ɗaukaka kansa gaba da su duka.
Et il ne se souciera point des dieux de ses pères, ni de l'amour des femmes, même il ne se souciera d'aucun Dieu; car il s'élèvera au-dessus de tout.
38 A maimakonsu, zai ɗaukaka allahn kagarai; allahn da kakanninsa ba su ko sani ba, shi ne zai miƙa masa zinariya, da azurfa, da duwatsu masu daraja, da abubuwa masu tsada.
Mais il honorera dans son lieu le dieu Mahuzzim, il honorera, dis-je, avec de l'or et de l'argent, et des pierres précieuses, et des choses désirables, le dieu que ses pères n'ont point connu.
39 Zai kai wa kagarai mafi ƙarfi hari da taimakon baƙon allah zai kuma girmama waɗanda suka yarda da shi zai ba su girma, ya kuma shugabantar da su a kan mutane da yawa, zai raba musu ƙasa ta zama ladansu.
Et il fera [de grands exploits] dans les forteresses les plus fortes, tenant le parti du dieu inconnu qu'il aura connu, il [leur] multipliera la gloire, et les fera dominer sur plusieurs, et leur partagera le pays à prix d'argent.
40 “A lokaci ƙarshe sarkin Kudu zai tasar masa da yaƙi, sarkin Arewa kuwa zai tunzura, yă tasar masa da kekunan yaƙi da mahayan dawakai, da jiragen ruwa da yawa. Zai ratsa ƙasashe, yă ci su da yaƙi, yă wuce.
Et au temps déterminé le Roi du Midi choquera avec lui de ses cornes mais le Roi de l'Aquilon se lèvera contre lui comme une tempête, avec des chariots et des gens de cheval, et avec plusieurs navires, et il entrera dans ses terres, et les inondera, et passera outre.
41 Zai kuma mamaye Kyakkyawa Ƙasa. Ƙasashe masu yawa za su fāɗi, amma Edom, Mowab da kuma shugabannin Ammon za su kuɓuta daga hannunsa.
Et il entrera au pays de noblesse, et plusieurs pays seront ruinés, mais ceux-ci réchapperont de sa main, [savoir], Edom, et Moab, et le principal lieu des enfants de Hammon.
42 Zai fadada mulkinsa har zuwa ƙasashe masu yawa; Masar ma ba za tă tsira ba.
Il mettra donc la main sur ces pays-là; et le pays d'Egypte n'échappera point.
43 Zai mallaki dukiyoyi na zinariya, da na azurfa, da dukan abubuwa masu tsada na Masar. Zai kuma ci Libiyawa da Kush da yaƙi.
Il se rendra maître des trésors d'or et d'argent, et de toutes les choses désirables de l'Egypte; les Libyens et ceux de Cus seront à sa suite.
44 Amma labari daga gabas da arewa za su firgita shi, shi kuwa zai ci gaba da yin yaƙi da zafi, yă karkashe mutane da yawa, yă shafe su.
Mais les nouvelles de l'Orient et de l'Aquilon le troubleront, et il sortira avec une grande fureur, pour détruire et exterminer beaucoup de gens.
45 Zai kafa tentin mulkinsa tsakanin tekunan da suke a kyakkyawan tsauni mai tsarki. Duk da haka zai zo ga ƙarshensa, kuma babu wanda zai taimake shi.
Et il dressera les tentes de sa maison royale entre les mers, à l'[opposite] de la noble montagne de la sainteté; mais il viendra à sa fin, et personne ne lui donnera du secours.

< Daniyel 11 >