< Daniyel 11 >

1 A shekara ta fari ta Dariyus mutumin Mede, na ɗauki matsayina domin in goyi baya in kuma kāre shi.)
Je suis celui qui, en la première année du règne de Cyrus, se tint près de lui pour le fortifier et l'affermir.
2 “Yanzu dai, zan faɗa maka gaskiya. Sarakuna uku za su taso a Farisa, sa’an nan kuma na huɗu, wanda zai fi dukansu dukiya. Sa’ad da zai sami iko saboda dukiyarsa, zai zuga dukan kowane mutum yă yi gāba da masarautar Girka.
Et maintenant je te ferai connaître la vérité: trois rois règneront encore sur la Perse; le quatrième prospèrera et les surpassera tous en richesses; et lorsqu'il sera en possession de ses richesses, il fera la guerre à tous les royaumes des Hellènes.
3 Sa’an nan wani babban sarki zai bayyana, wanda zai yi mulki da babban iko yă kuma yi abin da ya ga dama.
Et un roi puissant s'élèvera, et il sera maître d'un grand empire, et il fera ce qu'il voudra.
4 Bayan da ya bayyana, daularsa za tă wargaje za a rarraba ta zuwa kusurwoyi huɗu na duniya, a ba waɗansu waɗanda ba zuriyarsa ba, ba kuwa za su yi mulki da iko kamar yadda ya yi ba, gama za a tumɓuki daularsa a kuma ba wa waɗansu.
Et, au moment où son empire sera affermi, il sera brisé et partagé aux quatre vents du ciel; et il ne passera point à ses descendants, et il ne gardera point sa puissance selon ses désirs; car sa royauté lui sera arrachée; puis elle passera à d'autres après lui.
5 “Sai sarki Kudu zai yi ƙarfi ƙwarai, amma ɗaya daga cikin komandodinsa zai yi ƙarfi fiye da shi, zai kuma yi mulki masarautarsa da iko mai girma.
Et le roi du midi se fortifiera; mais l'un de ces princes prévaudra contre lui, et il dominera sur un grand royaume.
6 Bayan’yan shekaru, za su haɗa kai. Diyar sarkin Kudu za tă je wurin sarkin Arewa ta sada zumunci, amma ba za tă riƙe iko ba, shi kuwa da ikonsa ba za su daɗe ba. A waɗannan kwanaki za a bashe ta, da ita da masu rakiyarta da kuma mahaifinta da kuma wanda ya goyi bayanta.
Et quelques années après ils s'uniront; et la fille du roi du midi ira trouver le roi de l'aquilon pour faire alliance avec lui; mais elle ne retirera pas de là un bras puissant; et la race du vainqueur ne se maintiendra pas; et elle-même sera livrée avec ceux qui la conduisaient, et la jeune fille, et celui qui la fortifiait en ces temps.
7 “Wani daga cikin zuriyarta zai taso yă ɗauki matsayinta. Zai kai wa sojojin sarkin Arewa hari yă kuma shiga kagararsa; zai yi yaƙi da su yă kuma yi nasara.
Mais un rejeton de la fleur de sa racine s'élèvera bientôt après; et il s'avancera à la tête d'une armée, et il entrera dans les forteresses du roi de l'aquilon; il combattra contre elles, et il s'en rendra maître.
8 Zai ƙwace allolinsu, siffofinsu na ƙarfe da kuma kaya masu daraja na azurfa da na zinariya a kuma kai su Masar. Zai yi’yan shekaru bai kai wa sarkin Arewa yaƙi ba.
Et il transportera en Égypte, avec les captifs, leurs dieux et leurs statues de fonte et leurs objets précieux d'argent et d'or; et lui-même subsistera plus longtemps que le roi de l'aquilon.
9 Sa’an nan sarkin Arewa zai kai wa sarkin Kudu hari, amma zai janye, yă koma ƙasarsa.
Celui-ci à son tour entrera dans le royaume du roi du midi, puis il retournera en sa propre terre.
10 ’Ya’yansa maza za su yi shirin yaƙi za su kuma tattara babbar rundunar sojoji, waɗanda za su yi ta mamayewa kamar rigyawar da ba iya tarewa, kuma za su kai yaƙin har kagararsa.
Et ses fils parmi maintes nations rassembleront une grande multitude; et l'un d'eux se mettra en campagne; et en sa marche il s'avancera comme un torrent débordé; il passera, il campera et rassemblera, ses forces pour le combat.
11 “Sa’an nan sai sarkin Kudu zai kama hanya da fushi zuwa yaƙi da sarkin Arewa, wanda zai tattara babbar rundunar yaƙi, amma za a ci shi da yaƙi.
Et le roi du midi s'effarouchera, et il s'avancera pour combattre le roi de l'aquilon; et il lèvera une grande armée, et une grande multitude d'ennemis lui sera livrée.
12 Sa’ad da zai kawar da rundunar, sarkin Kudu zai cika da girman kai zai kuma kashe mutane dubbai, duk da haka ba zai kasance mai nasara ba.
Et il prendra captive cette multitude, et son cœur s'enorgueillira, et il massacrera des myriades d'ennemis; mais il n'en sera pas plus puissant.
13 Sarki Arewa kuma zai ƙara tara babbar rundunar soja, wadda ta fi ta dā girma; bayan waɗansu shekaru kuma, zai tafi yaƙi da babbar rundunar mayaƙa cike da kayan yaƙi.
Car le roi de l'aquilon reviendra, et il conduira des troupes en plus grand nombre que la première fois; et à la fin des temps et des années une armée envahissante arrivera avec une grande force et de grands approvisionnements.
14 “A waɗannan lokutan mutane da yawa za su tashi gāba da sarkin Kudu. Amma waɗansu’yan kama-karya za su taso daga jama’arka da niyya su cika abin da wahayin ya ce, amma za a fatattake su.
Et en ce temps-là plusieurs se soulèveront contre le roi du midi, et des fils de ton peuple s'élèveront comme un fléau pour accomplir une vision; mais ils manqueront de force.
15 Sa’an nan sarkin arewa zai zo ya gina mahaurai a jikin katagar birni don yă ci birnin da yaƙi. Sojojin nan na Kudu kuwa ba za su iya tsayawa ba, ko zaɓaɓɓun jarumawansu ma, gama za su rasa ƙarfin tsayawa.
Car le roi de l'aquilon s'avancera; il élèvera des terrasses; il prendra des villes fortes; et les bras du roi du midi soutiendront le choc, et ses troupes d'élite se lèveront; mais ils ne seront pas de force à résister.
16 Wanda ya kai harin zai yi yadda ya ga dama, ba wanda zai iya ja da shi. Zai kafa kansa a Kyakkyawar Ƙasa zai kuma sami ikon da zai hallaka ta.
Et le roi de l'aquilon, après l'avoir ainsi envahi, fera tout ce qu'il voudra, et nul ne tiendra devant lui. Et il s'arrêtera en la terre de Sabé; et il la détruira de sa main.
17 Zai yunƙura yă zo da ƙarfin dukan masarautarsa zai kuma nemi haɗinkan sarkin Kudu. Zai kuma ba shi diyarsa yă aura don yă lalatar da mulkin, amma shirinsa ba zai yi nasara ba ko yă taimake shi ba.
Et il tournera son visage pour entrer en forces dans le royaume du midi, et toutes choses prospèreront devant lui; il donnera au roi ennemi une fille des femmes pour le perdre; mais il n'y réussira point, et elle ne sera pas à lui.
18 Sa’an nan zai mai da hankalinsa zuwa ƙasashe a bakin kogi, zai kuma kama da yawansu, amma wani komanda zai kawo ƙarshen faɗin ransa, zai kuma sa faɗin ransa yă koma masa.
Alors il tournera son visage contre les îles, et il en prendra plusieurs; et il arrêtera d'abord les princes de son opprobre; mais son opprobre retombera sur lui.
19 Bayan wannan, zai juya ga kagarar ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe yă fāɗi, ba kuwa za a ƙara ganinsa ba.
Et il retournera son visage vers la force de sa terre; mais il sera affaibli, et il tombera, et on ne le retrouvera plus.
20 “Magājinsa zai aiki mai karɓar haraji don darajar masarautarsa. Amma ba da daɗewa ba za a hallaka shi, duk da haka ba da fushi ko cikin yaƙi ba.
Et de sa racine s'élèvera un rejeton qui sera comme un plant sur le trône qu'il occupait avec gloire. Et en ces jours-là il sera encore brisé, mais non en face, non dans un combat.
21 “Magājin wannan sarki zai zama wani mutumin banza wanda ma bai fito daga gidan sarauta ba. Zai taso ba zato ba tsammani, yă ƙwace sarautar ta hanyar zamba.
Un autre prendra sa place, qui sera méprisé; on ne lui aura point accordé les honneurs de la royauté; mais il viendra avec ruse, et à force d'artifices il se rendra maître du royaume,
22 Sa’an nan zai shafe mayaƙa masu yawa a gabansa; zai hallaka har da waɗanda suke mulki na alkawari.
Et les bras de son adversaire seront énervés devant sa face; ils seront brisés, ainsi que le chef de l'alliance.
23 Bayan ƙulla yarjejjeniya da shi, zai yi zamba cikin aminci, kuma zai sami damar hawan mulki da goyon baya mutane kaɗan.
Et après leur traité, il trompera encore celui-ci; il s'avancera, et prévaudra sur lui avec un petit nombre de troupes.
24 Sa’ad da yankuna mafi arziki suke ji kome lafiya yake, zai kai musu hari kuma Zai aikata abin da kakanninsa ba su taɓa yi ba. Zai rarraba abin da aka kwaso daga yaƙi, da ganima, da dukiya ga dukan mabiyansa. Zai kuma yi shiri yă kai wa mafaka hari, amma na ɗan lokaci ne kawai.
Il viendra en des régions paisibles et opulentes; et il fera ce que n'ont fait ni ses pères ni les pères de ses pères; il emportera leur butin, leurs dépouilles, leurs richesses, et il concevra de mauvais desseins contre l'Égypte; mais cela n'aura qu'un temps.
25 “Tare da babbar rundunar mayaƙa zai yi ƙarfin hali yă far wa sarkin Kudu da yaƙi. Sarkin kudu zai haɗa babbar rundunar soja mai ƙarfi don yaƙin, amma ba zai iya karo da shi ba, domin za a shirya masa maƙarƙashiya.
Et sa force et son cœur s'élèveront avec une grande force contre le roi du midi; et le roi du midi soutiendra aussi la guerre avec une force très grande et très redoutable; mais ses armées ne tiendront pas, parce que de mauvais desseins auront été formés contre lui.
26 Waɗanda suke ci daga tanadin sarki za su yi ƙoƙari su hallaka shi; za a share mayaƙansa, kuma za a kashe mutane masu yawa a yaƙin.
On mangera avec lui; puis on le brisera, et son ennemi engloutira ses armées, et les morts tomberont en foule.
27 Sarakunan nan biyu sun sa mugunta a ransu. Za su zauna a tebur guda su yi ta shara wa juna ƙarya, amma a banza, gama lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna.
Et les deux rois, le cœur plein de perversité, assis à la même table, se diront des mensonges; mais cela ne réussira pas, parce que leur fin arrivera au temps marqué.
28 “Sarkin Arewa zai koma ƙasarsa da dukiya mai girma, amma zuciyarsa za tă yi gāba da tsattsarkan alkawari. Zai ɗauki mataki a kan wannan abu sa’an nan yă koma ƙasarsa.
Et le roi de l'aquilon retournera en sa terre avec de grandes richesses; et son cœur sera opposé à l'alliance sainte, et il fera de grandes choses, et il rentrera dans son royaume.
29 “A ƙayyadadden lokaci zai sāke kai wa Kudu hari, amma a wannan karo abin da zai faru zai sha bamban daga abin da ya faru can baya.
Il reviendra au temps marqué, et marchera contre le midi; mais cette dernière invasion ne sera pas comme la première.
30 Jiragen ruwa yammancin bakin teku za su yi gāba da shi, zuciyarsa kuwa za tă yi sanyi. Sa’an nan zai juya ya huce haushinsa a kan tsattsarkan alkawari. Zai komo yă nuna jinƙai ga waɗanda suka juya wa tsattsarkan alkawari baya.
Les Citians, sortis de leurs pays, marcheront contre lui; et par eux il sera abaissé, et il battra en retraite; il s'irritera contre l'alliance sainte, et agira contre elle; puis il se remettra en campagne, et s'entendra avec ceux qui auront abandonné l'alliance sainte.
31 “Mayaƙansa za su taso su ƙazantar da kagarar haikali za su kuma kawar da hadaya ta kullum. Sa’an nan za su kafa abin banƙyama da yake lalatarwa.
Et des rejetons de lui s'élèveront, et ils profaneront le sanctuaire de la Toute-Puissance, et ils feront cesser le sacrifice perpétuel, et ils le remplaceront par l'abomination de la désolation.
32 Ta wurin daɗin baki zai gurɓata waɗannan da suka karya alkawari, amma mutanen da suka san Allahnsu za su yi tsayin daka su yi jayayya da shi.
Et les impies feront alliance entre eux pour faire le mal; mais un peuple connaissant son Dieu prévaudra et agira vaillamment.
33 “Waɗanda suke da hikima za su wayar da kan mutane da yawa, duk da haka za a kashe su da takobi, waɗansu da wuta, a washe waɗansu a kai su bauta.
Et les sages du peuple comprendront beaucoup de choses; toutefois ils seront affaiblis par le glaive, par le feu, par la captivité, et par un pillage qui durera bien des jours.
34 Sa’ad da suka fāɗi, za su sami ɗan taimako, mutane da yawa za su haɗa kai da su, amma da munafunci.
Et dans leur détresse ils recevront un faible secours; mais plusieurs se joindront à eux avec des vues perfides,
35 Waɗansu masu hikima za su yi tuntuɓe, don a tsabtacce su, a tsarkake su, su yi tsab, har matuƙar da aka ƙayyade ta yi.
Et parmi les sages quelques-uns auront beaucoup à souffrir pour être purifiés, élus et manifestés aux derniers jours; car ces choses doivent s'accomplir au temps marqué.
36 “Sarkin zai yi abin da ya ga dama. Zai ɗaukaka yă kuma girmama kansa gaba da kowane allah zai kuma faɗa munanan abubuwa a kan Allahn alloli. Zai yi nasara har sai lokacin hukunci ya cika, gama abin da aka ƙaddara zai cika.
Et le roi fera selon sa volonté; il s'élèvera, et il se glorifiera contre toute divinité, et il parlera un langage superbe, et il prospèrera jusqu'à ce que la colère de Dieu s'accomplisse; car cela doit finir ainsi.
37 Ba zai kula da alloli iyayensa ba ko wanda mata suke sha’awa, balle ma yă ga darajar wani allah, amma zai ɗaukaka kansa gaba da su duka.
Et il ne reconnaîtra aucun des dieux de ses pères; il sera épris des femmes, et ne reconnaîtra aucun dieu; car il se croira plus grand qu'eux tous.
38 A maimakonsu, zai ɗaukaka allahn kagarai; allahn da kakanninsa ba su ko sani ba, shi ne zai miƙa masa zinariya, da azurfa, da duwatsu masu daraja, da abubuwa masu tsada.
Et il honorera le dieu Maozim en son temple, et il le glorifiera en lui offrant de l'or, de l'argent, des pierres précieuses et des choses de prix, ce dieu que ses pères ne connaissaient pas.
39 Zai kai wa kagarai mafi ƙarfi hari da taimakon baƙon allah zai kuma girmama waɗanda suka yarda da shi zai ba su girma, ya kuma shugabantar da su a kan mutane da yawa, zai raba musu ƙasa ta zama ladansu.
Et il donnera place dans les forteresses de refuge à un dieu étranger; il multipliera ses honneurs; il lui assujettira beaucoup d'hommes, et il partagera la terre pour en faire des présents.
40 “A lokaci ƙarshe sarkin Kudu zai tasar masa da yaƙi, sarkin Arewa kuwa zai tunzura, yă tasar masa da kekunan yaƙi da mahayan dawakai, da jiragen ruwa da yawa. Zai ratsa ƙasashe, yă ci su da yaƙi, yă wuce.
Et au temps marqué il sera aux prises avec le roi du midi; et le roi de l'aquilon conduira contre lui une multitude de chars, de cavaliers, de vaisseaux, et il envahira sa terre, et il la traversera, et il la foulera aux pieds.
41 Zai kuma mamaye Kyakkyawa Ƙasa. Ƙasashe masu yawa za su fāɗi, amma Edom, Mowab da kuma shugabannin Ammon za su kuɓuta daga hannunsa.
Et il entrera dans la terre de Sébaïm, et beaucoup succomberont. Et voici ceux qui échapperont à sa main: Édom, Moab et la principauté des fils d'Ammon.
42 Zai fadada mulkinsa har zuwa ƙasashe masu yawa; Masar ma ba za tă tsira ba.
Et il étendra son bras sur la terre de Palestine, et l'Égypte ne sera pas sauvée.
43 Zai mallaki dukiyoyi na zinariya, da na azurfa, da dukan abubuwa masu tsada na Masar. Zai kuma ci Libiyawa da Kush da yaƙi.
Et il se rendra maître des lieux où sont cachés l'or et l'argent et tout ce qu'il y a de précieux en Égypte, en Libye et en Éthiopie, et dans leurs forteresses.
44 Amma labari daga gabas da arewa za su firgita shi, shi kuwa zai ci gaba da yin yaƙi da zafi, yă karkashe mutane da yawa, yă shafe su.
Puis des rumeurs, des nouvelles pressantes, de l'orient et du nord, le troubleront; et il viendra plein de colère pour exterminer beaucoup d'ennemis.
45 Zai kafa tentin mulkinsa tsakanin tekunan da suke a kyakkyawan tsauni mai tsarki. Duk da haka zai zo ga ƙarshensa, kuma babu wanda zai taimake shi.
Et il dressera les tentes de son palais entre les mers, sur la montagne sainte de Sébaïn, et il y viendra jusqu'à sa fin, et nul ne pourra le sauver.

< Daniyel 11 >