< Daniyel 11 >
1 A shekara ta fari ta Dariyus mutumin Mede, na ɗauki matsayina domin in goyi baya in kuma kāre shi.)
And I also, in the first year of Darius the Mede, stood up to confirm and strengthen him.
2 “Yanzu dai, zan faɗa maka gaskiya. Sarakuna uku za su taso a Farisa, sa’an nan kuma na huɗu, wanda zai fi dukansu dukiya. Sa’ad da zai sami iko saboda dukiyarsa, zai zuga dukan kowane mutum yă yi gāba da masarautar Girka.
And now I will tell thee what is true. Behold, there shall arise yet three kings in Persia, and the fourth shall be far richer than they all; and, relying upon his riches, he shall stir up all against the realm of Greece.
3 Sa’an nan wani babban sarki zai bayyana, wanda zai yi mulki da babban iko yă kuma yi abin da ya ga dama.
But a mighty king shall arise, and rule with great dominion, and do according to his will.
4 Bayan da ya bayyana, daularsa za tă wargaje za a rarraba ta zuwa kusurwoyi huɗu na duniya, a ba waɗansu waɗanda ba zuriyarsa ba, ba kuwa za su yi mulki da iko kamar yadda ya yi ba, gama za a tumɓuki daularsa a kuma ba wa waɗansu.
But when he shall have arisen, his kingdom shall be broken in pieces, and shall be divided toward the four winds of heaven; and not to his posterity, nor with the dominion with which he ruled; for his kingdom shall be plucked up, and divided amongst others besides those.
5 “Sai sarki Kudu zai yi ƙarfi ƙwarai, amma ɗaya daga cikin komandodinsa zai yi ƙarfi fiye da shi, zai kuma yi mulki masarautarsa da iko mai girma.
And the king of the South shall become strong; but one of his princes shall become stronger than he, and have dominion; his dominion shall be a great dominion.
6 Bayan’yan shekaru, za su haɗa kai. Diyar sarkin Kudu za tă je wurin sarkin Arewa ta sada zumunci, amma ba za tă riƙe iko ba, shi kuwa da ikonsa ba za su daɗe ba. A waɗannan kwanaki za a bashe ta, da ita da masu rakiyarta da kuma mahaifinta da kuma wanda ya goyi bayanta.
And after some years they shall ally themselves with each other; and the daughter of the king of the South shall come to the king of the North, to make peace; but she shall not retain the power of giving aid; neither shall he stand, nor his aid; but she shall be given up, and they that caused her to go, and he that begat her, and he that received her in those times.
7 “Wani daga cikin zuriyarta zai taso yă ɗauki matsayinta. Zai kai wa sojojin sarkin Arewa hari yă kuma shiga kagararsa; zai yi yaƙi da su yă kuma yi nasara.
But from a shoot of her roots shall one arise in his place, who shall come to an army, and shall come against the fortresses of the king of the North, and shall deal with them according to his pleasure, and prevail against them.
8 Zai ƙwace allolinsu, siffofinsu na ƙarfe da kuma kaya masu daraja na azurfa da na zinariya a kuma kai su Masar. Zai yi’yan shekaru bai kai wa sarkin Arewa yaƙi ba.
And their gods, with their molten images, and their precious vessels of silver and of gold, shall he carry into captivity into Egypt; then shall he stand away for many years from the king of the North;
9 Sa’an nan sarkin Arewa zai kai wa sarkin Kudu hari, amma zai janye, yă koma ƙasarsa.
and he shall come against the kingdom of the king of the South, but he shall return into his own land.
10 ’Ya’yansa maza za su yi shirin yaƙi za su kuma tattara babbar rundunar sojoji, waɗanda za su yi ta mamayewa kamar rigyawar da ba iya tarewa, kuma za su kai yaƙin har kagararsa.
But his sons shall be stirred up, and shall assemble a multitude of large forces; and one of them shall move onward, and overflow, and pass through, and shall again stir himself up to carry on the war even to his stronghold.
11 “Sa’an nan sai sarkin Kudu zai kama hanya da fushi zuwa yaƙi da sarkin Arewa, wanda zai tattara babbar rundunar yaƙi, amma za a ci shi da yaƙi.
Then shall the king of the South be enraged, and shall come forth and fight with him, even with the king of the North; and shall lead forth a great multitude, and the multitude shall be given into his hand.
12 Sa’ad da zai kawar da rundunar, sarkin Kudu zai cika da girman kai zai kuma kashe mutane dubbai, duk da haka ba zai kasance mai nasara ba.
And the multitude shall be elated, and his heart shall be lifted up, and he shall cast down tens of thousands; but he shall not be strong.
13 Sarki Arewa kuma zai ƙara tara babbar rundunar soja, wadda ta fi ta dā girma; bayan waɗansu shekaru kuma, zai tafi yaƙi da babbar rundunar mayaƙa cike da kayan yaƙi.
For the king of the North shall return and raise up against him a multitude greater than the former, and shall steadily come after certain years with a great army and with great riches.
14 “A waɗannan lokutan mutane da yawa za su tashi gāba da sarkin Kudu. Amma waɗansu’yan kama-karya za su taso daga jama’arka da niyya su cika abin da wahayin ya ce, amma za a fatattake su.
And in those times many will stand up against the king of the South; and violent men of thy people shall exalt themselves, so as to establish the vision, and shall fall.
15 Sa’an nan sarkin arewa zai zo ya gina mahaurai a jikin katagar birni don yă ci birnin da yaƙi. Sojojin nan na Kudu kuwa ba za su iya tsayawa ba, ko zaɓaɓɓun jarumawansu ma, gama za su rasa ƙarfin tsayawa.
And the king of the North shall come, and cast up a mound, and take a fortified city; and the arms of the South shall not withstand, neither his chosen men, neither shall there be any strength to withstand.
16 Wanda ya kai harin zai yi yadda ya ga dama, ba wanda zai iya ja da shi. Zai kafa kansa a Kyakkyawar Ƙasa zai kuma sami ikon da zai hallaka ta.
And he that cometh against him shall do according to his will, and none shall stand before him; and he shall stand in the beautiful land, and destruction shall be in his hand.
17 Zai yunƙura yă zo da ƙarfin dukan masarautarsa zai kuma nemi haɗinkan sarkin Kudu. Zai kuma ba shi diyarsa yă aura don yă lalatar da mulkin, amma shirinsa ba zai yi nasara ba ko yă taimake shi ba.
And he shall set his face to come with the strength of his whole kingdom, and shall make pacification with him; and he shall give him his daughter in marriage, to ruin his dominion. But it shall not succeed, neither shall it be for him.
18 Sa’an nan zai mai da hankalinsa zuwa ƙasashe a bakin kogi, zai kuma kama da yawansu, amma wani komanda zai kawo ƙarshen faɗin ransa, zai kuma sa faɗin ransa yă koma masa.
After this he shall turn his face to the isles, and shall take many; but a commander shall put an end to his scorn; nay, shall cause his scorn to return upon himself.
19 Bayan wannan, zai juya ga kagarar ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe yă fāɗi, ba kuwa za a ƙara ganinsa ba.
Then shall he turn his face to the strongholds of his own land; and he shall stumble, and fall, and shall not be found.
20 “Magājinsa zai aiki mai karɓar haraji don darajar masarautarsa. Amma ba da daɗewa ba za a hallaka shi, duk da haka ba da fushi ko cikin yaƙi ba.
Then shall arise in his place one who shall send an exacter of tribute through the glory of his kingdom; but within few days shall he be destroyed, neither by anger nor by battle.
21 “Magājin wannan sarki zai zama wani mutumin banza wanda ma bai fito daga gidan sarauta ba. Zai taso ba zato ba tsammani, yă ƙwace sarautar ta hanyar zamba.
And in his place shall arise a despised person, to whom they shall not give the honor of the kingdom; but in the midst of peace he shall come in and obtain the kingdom by flatteries.
22 Sa’an nan zai shafe mayaƙa masu yawa a gabansa; zai hallaka har da waɗanda suke mulki na alkawari.
And the forces of a flood shall be overwhelmed before him, and shall be broken in pieces; and even the prince that is allied with him.
23 Bayan ƙulla yarjejjeniya da shi, zai yi zamba cikin aminci, kuma zai sami damar hawan mulki da goyon baya mutane kaɗan.
For after making a league with him, he will practise deceit; for he will come up, and prevail with a small people.
24 Sa’ad da yankuna mafi arziki suke ji kome lafiya yake, zai kai musu hari kuma Zai aikata abin da kakanninsa ba su taɓa yi ba. Zai rarraba abin da aka kwaso daga yaƙi, da ganima, da dukiya ga dukan mabiyansa. Zai kuma yi shiri yă kai wa mafaka hari, amma na ɗan lokaci ne kawai.
In the midst of security shall he come into the fattest provinces of the land, and he shall do what his fathers never did, nor his fathers' fathers; he shall scatter among them prey, and spoil, and riches; and he shall form his devices against the strongholds, even to a set time.
25 “Tare da babbar rundunar mayaƙa zai yi ƙarfin hali yă far wa sarkin Kudu da yaƙi. Sarkin kudu zai haɗa babbar rundunar soja mai ƙarfi don yaƙin, amma ba zai iya karo da shi ba, domin za a shirya masa maƙarƙashiya.
And he shall stir up his power and his courage against the king of the South, with a great army; and the king of the South shall be stirred up to battle with a very great and mighty army; but he shall not stand, for they shall form devices against him.
26 Waɗanda suke ci daga tanadin sarki za su yi ƙoƙari su hallaka shi; za a share mayaƙansa, kuma za a kashe mutane masu yawa a yaƙin.
Even they that eat of his own food shall destroy him; and his army shall overflow, and many shall fall down slain.
27 Sarakunan nan biyu sun sa mugunta a ransu. Za su zauna a tebur guda su yi ta shara wa juna ƙarya, amma a banza, gama lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna.
And the hearts of both these kings shall be to do mischief; and at one table shall they speak lies; but it shall not prosper; for yet the end is for the appointed time.
28 “Sarkin Arewa zai koma ƙasarsa da dukiya mai girma, amma zuciyarsa za tă yi gāba da tsattsarkan alkawari. Zai ɗauki mataki a kan wannan abu sa’an nan yă koma ƙasarsa.
Then shall he return into his land with great riches; and he will set his heart against the holy covenant, and he will execute his purposes, and return to his own land.
29 “A ƙayyadadden lokaci zai sāke kai wa Kudu hari, amma a wannan karo abin da zai faru zai sha bamban daga abin da ya faru can baya.
At the appointed time he shall again go against the South; but the second time it shall not be as at the first.
30 Jiragen ruwa yammancin bakin teku za su yi gāba da shi, zuciyarsa kuwa za tă yi sanyi. Sa’an nan zai juya ya huce haushinsa a kan tsattsarkan alkawari. Zai komo yă nuna jinƙai ga waɗanda suka juya wa tsattsarkan alkawari baya.
For the Chittaean ships shall come against him, and he shall be discouraged, and return, and be enraged against the holy covenant, and execute his purposes; and he shall again have an understanding with them that forsake the holy covenant.
31 “Mayaƙansa za su taso su ƙazantar da kagarar haikali za su kuma kawar da hadaya ta kullum. Sa’an nan za su kafa abin banƙyama da yake lalatarwa.
And forces shall be raised by him, which shall pollute the sanctuary, the stronghold, and take away the daily sacrifice, and set up the abomination of the destroyer.
32 Ta wurin daɗin baki zai gurɓata waɗannan da suka karya alkawari, amma mutanen da suka san Allahnsu za su yi tsayin daka su yi jayayya da shi.
And such as do wickedly against the covenant will he lead to apostasy by flatteries; but the people that know their God shall be strong, and do exploits.
33 “Waɗanda suke da hikima za su wayar da kan mutane da yawa, duk da haka za a kashe su da takobi, waɗansu da wuta, a washe waɗansu a kai su bauta.
And they that have understanding among the people shall instruct many; but they shall fall by the sword, and by flame, by captivity, and by spoil, many days.
34 Sa’ad da suka fāɗi, za su sami ɗan taimako, mutane da yawa za su haɗa kai da su, amma da munafunci.
And whilst they fall they shall receive a little help, and many shall join themselves to them with flatteries.
35 Waɗansu masu hikima za su yi tuntuɓe, don a tsabtacce su, a tsarkake su, su yi tsab, har matuƙar da aka ƙayyade ta yi.
And some of them of understanding shall fall, to try them, and to purify, and cleanse, even to the time of the end, for it is yet at the time appointed.
36 “Sarkin zai yi abin da ya ga dama. Zai ɗaukaka yă kuma girmama kansa gaba da kowane allah zai kuma faɗa munanan abubuwa a kan Allahn alloli. Zai yi nasara har sai lokacin hukunci ya cika, gama abin da aka ƙaddara zai cika.
And the king shall do according to his will; and he will exalt himself and magnify himself against every god, and he will speak horrible things against the God of gods, and he will prosper until the indignation be accomplished; for that which is determined shall be done.
37 Ba zai kula da alloli iyayensa ba ko wanda mata suke sha’awa, balle ma yă ga darajar wani allah, amma zai ɗaukaka kansa gaba da su duka.
Neither will he regard the god of his fathers, nor the desire of women; nor will he regard any god, but he will magnify himself against all.
38 A maimakonsu, zai ɗaukaka allahn kagarai; allahn da kakanninsa ba su ko sani ba, shi ne zai miƙa masa zinariya, da azurfa, da duwatsu masu daraja, da abubuwa masu tsada.
But in their place will he honor the god of strongholds, even the god whom his fathers knew not shall he honor with gold, and with silver, and with precious stones, and with jewels.
39 Zai kai wa kagarai mafi ƙarfi hari da taimakon baƙon allah zai kuma girmama waɗanda suka yarda da shi zai ba su girma, ya kuma shugabantar da su a kan mutane da yawa, zai raba musu ƙasa ta zama ladansu.
And he shall do his will against fenced strongholds with a strange god; whoever acknowledge him, to them he will give great honor, and give them dominion over many, and divide the land amongst them for a reward.
40 “A lokaci ƙarshe sarkin Kudu zai tasar masa da yaƙi, sarkin Arewa kuwa zai tunzura, yă tasar masa da kekunan yaƙi da mahayan dawakai, da jiragen ruwa da yawa. Zai ratsa ƙasashe, yă ci su da yaƙi, yă wuce.
But at the time of the end shall the king of the South push at him, and the king of the North shall rush against him like a whirlwind with chariots, and with horsemen, and with many ships; and he shall enter into the countries, and overflow them, and pass over them.
41 Zai kuma mamaye Kyakkyawa Ƙasa. Ƙasashe masu yawa za su fāɗi, amma Edom, Mowab da kuma shugabannin Ammon za su kuɓuta daga hannunsa.
He shall also enter into the beautiful land, and multitudes shall be overthrown; but these shall escape out of his hand, Edom, and Moab, and the chief of the sons of Ammon.
42 Zai fadada mulkinsa har zuwa ƙasashe masu yawa; Masar ma ba za tă tsira ba.
He shall stretch forth his hand also upon the countries, and the land of Egypt shall not escape.
43 Zai mallaki dukiyoyi na zinariya, da na azurfa, da dukan abubuwa masu tsada na Masar. Zai kuma ci Libiyawa da Kush da yaƙi.
And he shall have power over the treasures of gold and of silver, and over all the precious things of Egypt; and the Lybians and Ethiopians shall be in his train.
44 Amma labari daga gabas da arewa za su firgita shi, shi kuwa zai ci gaba da yin yaƙi da zafi, yă karkashe mutane da yawa, yă shafe su.
But tidings out of the East and out of the North shall trouble him, and he shall go forth with great fury to destroy and utterly to take away many.
45 Zai kafa tentin mulkinsa tsakanin tekunan da suke a kyakkyawan tsauni mai tsarki. Duk da haka zai zo ga ƙarshensa, kuma babu wanda zai taimake shi.
And he shall pitch his palace-tents between the sea and the beautiful holy mountain; but he shall come to his end, and none shall help him.