< Daniyel 11 >

1 A shekara ta fari ta Dariyus mutumin Mede, na ɗauki matsayina domin in goyi baya in kuma kāre shi.)
“And so, from the first year of Darius the Mede, I stood firm, so that he might be reinforced and strengthened.
2 “Yanzu dai, zan faɗa maka gaskiya. Sarakuna uku za su taso a Farisa, sa’an nan kuma na huɗu, wanda zai fi dukansu dukiya. Sa’ad da zai sami iko saboda dukiyarsa, zai zuga dukan kowane mutum yă yi gāba da masarautar Girka.
And now I will announce to you the truth. Behold, up to a certain point, three kings will stand in Persia, and the fourth will be exceedingly enriched in power above them all. And when he has grown strong by his resources, he will stir up all against the kingdom of Greece.
3 Sa’an nan wani babban sarki zai bayyana, wanda zai yi mulki da babban iko yă kuma yi abin da ya ga dama.
But there will rise up a strong king, and he will rule with great power, and he will do what he pleases.
4 Bayan da ya bayyana, daularsa za tă wargaje za a rarraba ta zuwa kusurwoyi huɗu na duniya, a ba waɗansu waɗanda ba zuriyarsa ba, ba kuwa za su yi mulki da iko kamar yadda ya yi ba, gama za a tumɓuki daularsa a kuma ba wa waɗansu.
And when he has been firmly established, his kingdom will be shattered and will be divided towards the four winds of the heaven, but not to his posterity, nor according to his power with which he ruled. For his kingdom will be torn to pieces, even for the outsiders who have been expelled from these.
5 “Sai sarki Kudu zai yi ƙarfi ƙwarai, amma ɗaya daga cikin komandodinsa zai yi ƙarfi fiye da shi, zai kuma yi mulki masarautarsa da iko mai girma.
And the king of the South will be reinforced, yet one of his leaders will prevail over him, and he will rule with riches, for great is his domain.
6 Bayan’yan shekaru, za su haɗa kai. Diyar sarkin Kudu za tă je wurin sarkin Arewa ta sada zumunci, amma ba za tă riƙe iko ba, shi kuwa da ikonsa ba za su daɗe ba. A waɗannan kwanaki za a bashe ta, da ita da masu rakiyarta da kuma mahaifinta da kuma wanda ya goyi bayanta.
And after the end of years, they will form a federation, and the daughter of the king of the South will come to the king of the North to make friendship, but she will not obtain the strength of arms, neither will her offspring stand firm, and she will be handed over, along with those who brought her, her young men, and those who comforted her in these times.
7 “Wani daga cikin zuriyarta zai taso yă ɗauki matsayinta. Zai kai wa sojojin sarkin Arewa hari yă kuma shiga kagararsa; zai yi yaƙi da su yă kuma yi nasara.
And a transplant from the germination of her roots will stand up, and he will come with an army, and will enter into the province of the king of the North, and he will abuse them, and will hold it fast.
8 Zai ƙwace allolinsu, siffofinsu na ƙarfe da kuma kaya masu daraja na azurfa da na zinariya a kuma kai su Masar. Zai yi’yan shekaru bai kai wa sarkin Arewa yaƙi ba.
And, in addition, he will carry away captive into Egypt their gods, and their graven images, and likewise their precious vessels of gold and silver. He will prevail against the king of the North.
9 Sa’an nan sarkin Arewa zai kai wa sarkin Kudu hari, amma zai janye, yă koma ƙasarsa.
And the king of the South will enter into the kingdom, and will return to his own land.
10 ’Ya’yansa maza za su yi shirin yaƙi za su kuma tattara babbar rundunar sojoji, waɗanda za su yi ta mamayewa kamar rigyawar da ba iya tarewa, kuma za su kai yaƙin har kagararsa.
But his sons will be challenged, and they will assemble a multitude of very many forces. And he will arrive rushing and overflowing. And he will be turned back, and he will be enraged, and he will join the battle in his redness.
11 “Sa’an nan sai sarkin Kudu zai kama hanya da fushi zuwa yaƙi da sarkin Arewa, wanda zai tattara babbar rundunar yaƙi, amma za a ci shi da yaƙi.
And the king of the South, having being challenged, will go forth and will fight against the king of the North, and he will prepare an exceedingly great multitude, and a multitude will be given into his hand.
12 Sa’ad da zai kawar da rundunar, sarkin Kudu zai cika da girman kai zai kuma kashe mutane dubbai, duk da haka ba zai kasance mai nasara ba.
And he will seize a multitude, and his heart will be exalted, and he will cast down many thousands, but he will not prevail.
13 Sarki Arewa kuma zai ƙara tara babbar rundunar soja, wadda ta fi ta dā girma; bayan waɗansu shekaru kuma, zai tafi yaƙi da babbar rundunar mayaƙa cike da kayan yaƙi.
For the king of the North will change strategy and will prepare a multitude much greater than before, and at the end of times and years, he will rush forward with a great army and exceedingly great resources.
14 “A waɗannan lokutan mutane da yawa za su tashi gāba da sarkin Kudu. Amma waɗansu’yan kama-karya za su taso daga jama’arka da niyya su cika abin da wahayin ya ce, amma za a fatattake su.
And in those times, many will rise up against the king of the South. And likewise the sons of the deceivers among your people will extol themselves, so as to fulfill the vision, and they will collapse.
15 Sa’an nan sarkin arewa zai zo ya gina mahaurai a jikin katagar birni don yă ci birnin da yaƙi. Sojojin nan na Kudu kuwa ba za su iya tsayawa ba, ko zaɓaɓɓun jarumawansu ma, gama za su rasa ƙarfin tsayawa.
And the king of the North will arrive and will transport siege works, and he will seize the most fortified cities. And the arms of the South will not withstand him, and his elect will rise up to resist, but the strength will not.
16 Wanda ya kai harin zai yi yadda ya ga dama, ba wanda zai iya ja da shi. Zai kafa kansa a Kyakkyawar Ƙasa zai kuma sami ikon da zai hallaka ta.
And when he arrives, he will do just as he pleases, and there will be none who stand against his face. And he will stand in the illustrious land, and it will be consumed by his hand.
17 Zai yunƙura yă zo da ƙarfin dukan masarautarsa zai kuma nemi haɗinkan sarkin Kudu. Zai kuma ba shi diyarsa yă aura don yă lalatar da mulkin, amma shirinsa ba zai yi nasara ba ko yă taimake shi ba.
And he will set his face to strive to hold his entire kingdom, and he will make fair conditions with him. And he will give him a daughter among women, so as to overthrow it. But she will not stand, neither will she be for him.
18 Sa’an nan zai mai da hankalinsa zuwa ƙasashe a bakin kogi, zai kuma kama da yawansu, amma wani komanda zai kawo ƙarshen faɗin ransa, zai kuma sa faɗin ransa yă koma masa.
And he will turn his face towards the islands, and he will seize many. And he will cause the leader of his reproach to cease, and his reproach will be turned around for him.
19 Bayan wannan, zai juya ga kagarar ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe yă fāɗi, ba kuwa za a ƙara ganinsa ba.
And he will turn his face to the empire of his own land, and he will strike, and will overthrow, but he will not succeed.
20 “Magājinsa zai aiki mai karɓar haraji don darajar masarautarsa. Amma ba da daɗewa ba za a hallaka shi, duk da haka ba da fushi ko cikin yaƙi ba.
And there will stand up in his place one who is most worthless and unworthy of kingly honor. And in a short time, he will be worn out, but not in fury, nor in battle.
21 “Magājin wannan sarki zai zama wani mutumin banza wanda ma bai fito daga gidan sarauta ba. Zai taso ba zato ba tsammani, yă ƙwace sarautar ta hanyar zamba.
And there will stand up in his place the despicable one, and he will not be assigned the honor of a king. And he will arrive in secret, and he will obtain the kingdom by deceitfulness.
22 Sa’an nan zai shafe mayaƙa masu yawa a gabansa; zai hallaka har da waɗanda suke mulki na alkawari.
And the arms of the fighting will be assaulted before his face and will be shattered, and, in addition, the leader of the federation.
23 Bayan ƙulla yarjejjeniya da shi, zai yi zamba cikin aminci, kuma zai sami damar hawan mulki da goyon baya mutane kaɗan.
And, after making friends, he will trick him, and he will go up and will overcome with a small people.
24 Sa’ad da yankuna mafi arziki suke ji kome lafiya yake, zai kai musu hari kuma Zai aikata abin da kakanninsa ba su taɓa yi ba. Zai rarraba abin da aka kwaso daga yaƙi, da ganima, da dukiya ga dukan mabiyansa. Zai kuma yi shiri yă kai wa mafaka hari, amma na ɗan lokaci ne kawai.
And he will enter into rich and resourceful cities, and he will do what his fathers never did, nor his fathers’ fathers. He will scatter their spoils, and their prey, and their riches, and will form a plan against the most steadfast, and this until a time.
25 “Tare da babbar rundunar mayaƙa zai yi ƙarfin hali yă far wa sarkin Kudu da yaƙi. Sarkin kudu zai haɗa babbar rundunar soja mai ƙarfi don yaƙin, amma ba zai iya karo da shi ba, domin za a shirya masa maƙarƙashiya.
And his strength and his heart will be enraged against the king of the South with a great army. And the king of the South will be provoked into going to war by having many allies and exceedingly good circumstances, and yet these will not stand, for they will form plans against him.
26 Waɗanda suke ci daga tanadin sarki za su yi ƙoƙari su hallaka shi; za a share mayaƙansa, kuma za a kashe mutane masu yawa a yaƙin.
And those who eat bread with him will crush him, and his army will be suppressed, and very many will die, having been executed.
27 Sarakunan nan biyu sun sa mugunta a ransu. Za su zauna a tebur guda su yi ta shara wa juna ƙarya, amma a banza, gama lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna.
And the heart of two kings will be similar, to do harm, and they will speak lies at one table, but they will not succeed, because as yet the end is for another time.
28 “Sarkin Arewa zai koma ƙasarsa da dukiya mai girma, amma zuciyarsa za tă yi gāba da tsattsarkan alkawari. Zai ɗauki mataki a kan wannan abu sa’an nan yă koma ƙasarsa.
And he will return to his land with many resources. And his heart will be against the holy testament, and he will act, and he will return to his own land.
29 “A ƙayyadadden lokaci zai sāke kai wa Kudu hari, amma a wannan karo abin da zai faru zai sha bamban daga abin da ya faru can baya.
At the appointed time, he will return, and he will approach the South, but the latter time will not be like the former.
30 Jiragen ruwa yammancin bakin teku za su yi gāba da shi, zuciyarsa kuwa za tă yi sanyi. Sa’an nan zai juya ya huce haushinsa a kan tsattsarkan alkawari. Zai komo yă nuna jinƙai ga waɗanda suka juya wa tsattsarkan alkawari baya.
And the Greek warships and the Romans will come upon him, and he will be pierced, and will retreat, and will have scorn against the testament of the sanctuary, and he will act. And he will return and will consult their adversaries, who have forsaken the covenant of the sanctuary.
31 “Mayaƙansa za su taso su ƙazantar da kagarar haikali za su kuma kawar da hadaya ta kullum. Sa’an nan za su kafa abin banƙyama da yake lalatarwa.
And arms will take his side, and they will pollute the sanctuary of the strength, and they will take away the continual sacrifice and will replace it with the abomination of desolation.
32 Ta wurin daɗin baki zai gurɓata waɗannan da suka karya alkawari, amma mutanen da suka san Allahnsu za su yi tsayin daka su yi jayayya da shi.
And the impious within the testament will imitate deceitfully, but the people, knowing their God, will persevere and will act.
33 “Waɗanda suke da hikima za su wayar da kan mutane da yawa, duk da haka za a kashe su da takobi, waɗansu da wuta, a washe waɗansu a kai su bauta.
And the teachers among the people will teach many, but they will be ruined by the sword, and by fire, and by captivity, and by assaults for many days.
34 Sa’ad da suka fāɗi, za su sami ɗan taimako, mutane da yawa za su haɗa kai da su, amma da munafunci.
And when they have fallen, they will be supported with a little help, but many will apply to them deceitfully.
35 Waɗansu masu hikima za su yi tuntuɓe, don a tsabtacce su, a tsarkake su, su yi tsab, har matuƙar da aka ƙayyade ta yi.
And some of the learned will be ruined, that they may be kindled and chosen and purified, up to the predetermined time, because there will be still another time.
36 “Sarkin zai yi abin da ya ga dama. Zai ɗaukaka yă kuma girmama kansa gaba da kowane allah zai kuma faɗa munanan abubuwa a kan Allahn alloli. Zai yi nasara har sai lokacin hukunci ya cika, gama abin da aka ƙaddara zai cika.
And the king will act according to his will, and he will be lifted up and will be extolled against every god. And he will speak great things against the God of gods, and he will control, until the passion is completed. Once accomplished, the limit is reached with certainty.
37 Ba zai kula da alloli iyayensa ba ko wanda mata suke sha’awa, balle ma yă ga darajar wani allah, amma zai ɗaukaka kansa gaba da su duka.
And he will give no thought to the God of his fathers, and he will be in the desire of women, and he will not attend to any gods, because he will rise up against all things.
38 A maimakonsu, zai ɗaukaka allahn kagarai; allahn da kakanninsa ba su ko sani ba, shi ne zai miƙa masa zinariya, da azurfa, da duwatsu masu daraja, da abubuwa masu tsada.
But he will do homage to the god Maozim in his place, and, a god whom his fathers did not know, he will worship with gold, and silver, and precious stones, and costly things.
39 Zai kai wa kagarai mafi ƙarfi hari da taimakon baƙon allah zai kuma girmama waɗanda suka yarda da shi zai ba su girma, ya kuma shugabantar da su a kan mutane da yawa, zai raba musu ƙasa ta zama ladansu.
And he will act to reinforce Maozim with an alien god, of whom he has become aware, and he will increase their glory, and will give them power over many, and he will distribute land for free.
40 “A lokaci ƙarshe sarkin Kudu zai tasar masa da yaƙi, sarkin Arewa kuwa zai tunzura, yă tasar masa da kekunan yaƙi da mahayan dawakai, da jiragen ruwa da yawa. Zai ratsa ƙasashe, yă ci su da yaƙi, yă wuce.
And, at the predetermined time, the king of the South will fight against him, and the king of the North will come against him like a tempest, with chariots, and with horsemen, and with a great fleet, and he will enter into the lands, and will crush and pass through.
41 Zai kuma mamaye Kyakkyawa Ƙasa. Ƙasashe masu yawa za su fāɗi, amma Edom, Mowab da kuma shugabannin Ammon za su kuɓuta daga hannunsa.
And he will enter into the glorious land, and many will fall. But only these will be saved from his hand: Edom, and Moab, and the first part of the sons of Ammon.
42 Zai fadada mulkinsa har zuwa ƙasashe masu yawa; Masar ma ba za tă tsira ba.
And he will cast his hand upon the lands, and the land of Egypt will not escape.
43 Zai mallaki dukiyoyi na zinariya, da na azurfa, da dukan abubuwa masu tsada na Masar. Zai kuma ci Libiyawa da Kush da yaƙi.
And he will rule over the treasure chests of gold, and silver, and all the precious things of Egypt, and likewise he will pass through Libya and Ethiopia.
44 Amma labari daga gabas da arewa za su firgita shi, shi kuwa zai ci gaba da yin yaƙi da zafi, yă karkashe mutane da yawa, yă shafe su.
And rumors from the East and from the North will trouble him. And he will arrive with a great multitude to destroy and to execute many.
45 Zai kafa tentin mulkinsa tsakanin tekunan da suke a kyakkyawan tsauni mai tsarki. Duk da haka zai zo ga ƙarshensa, kuma babu wanda zai taimake shi.
And he will fasten his tabernacle, Apadno, between the seas, upon an illustrious and holy mountain, and he will come even to its summit, and no one will help him.”

< Daniyel 11 >