< Daniyel 10 >

1 A shekara ta uku ta Sairus sarkin Farisa, sai aka ba wa Daniyel (wanda ake kira Belteshazar) wahayi. Saƙon kuwa gaskiya ce wadda take tattare da babban yaƙi. Fahimtar saƙon ya zo masa a cikin wahayi.
در سال سوم کورش پادشاه فارس، امری بر دانیال که به بلطشصر مسمی بود کشف گردید و آن امر صحیح و مشقت عظیمی بود. پس امر را فهمید و رویا را دانست.۱
2 A wannan lokaci ni Daniyel na yi makoki har na sati uku.
در آن ایام من دانیال سه هفته تمام ماتم گرفتم.۲
3 Ban ci abinci mai kyau ba; ba nama ko ruwa inabin da ya shiga bakina; kuma ba na amfani da man shafawa gaba ɗaya har sai da sati nan uku suka wuce.
خوراک لذیذ نخوردم و گوشت و شراب به دهانم داخل نشد و تا انقضای آن سه هفته خویشتن را تدهین ننمودم.۳
4 A rana ta ashirin da huɗu ga watan farko, a sa’ad da nake tsaye a bakin babban kogi, Tigris,
و در روز بیست وچهارم ماه اول من بر کنار نهر عظیم یعنی دجله بودم.۴
5 na ɗaga kaina na duba sai ga wani mutum tsaye sanye da rigar lilin, ya yi ɗamara da zinariya zalla daga Ufaz kewaye da ƙugunsa.
و چشمان خود را برافراشته دیدم که ناگاه مردی ملبس به کتان که کمربندی از طلای اوفازبر کمر خود داشت،۵
6 Jikinsa kamar lu’ulu’u yake, fuskarsa kuma kamar walƙiya, idanunsa kamar harshen wuta, hannuwansa da ƙafafunsa kamar gogaggiyar tagulla, muryarsa kuma kamar amon babban taron jama’a.
و جسد او مثل زبرجد وروی وی مانند برق و چشمانش مثل شعله های آتش و بازوها و پایهایش مانند رنگ برنج صیقلی و آواز کلام او مثل صدای گروه عظیمی بود.۶
7 Ni, Daniyel, kaɗai ne na ga wahayin; mutanen da suke tare da ni ba su gani ba, amma wata irin babbar razana ta auko musu har suka gudu suka ɓuya.
و من دانیال تنها آن رویا را دیدم و کسانی که همراه من بودند رویا را ندیدند لیکن لرزش عظیمی بر ایشان مستولی شد و فرار کرده، خودرا پنهان کردند.۷
8 Sai aka bar ni ni kaɗai, ina juyayi wannan babban wahayi, ba ni da sauran ƙarfi, fuskata ta yamutse kuma ba ni da sauran ƙarfi.
و من تنها ماندم و آن رویای عظیم را مشاهده می‌نمودم و قوت در من باقی نماند و خرمی من به پژمردگی مبدل گردید ودیگر هیچ طاقت نداشتم.۸
9 Sai na ji yana magana, da ina sauraronsa, sai na shiga barci mai nauyi, na kuwa fāɗi rubda ciki.
اما آواز سخنانش راشنیدم و چون آواز کلام او را شنیدم به روی خودبر زمین افتاده، بیهوش گردیدم.۹
10 Sai hannu ya taɓa ni ya sa makyarkyata a hannuna da ƙafafuna.
که ناگاه دستی مرا لمس نمود و مرا بر دو زانو و کف دستهایم برخیزانید.۱۰
11 Sai ya ce, “Daniyel, kai ne wanda ake ƙauna sosai, ka yi lura da kyau game da kalmomin da zan yi maka magana a kansu, ka tashi yanzu, gama an aiko ni a gare ka.” Sa’ad da ya faɗa mini haka, sai na tashi a tsaye ina rawan jiki.
و او مرا گفت: «ای دانیال مرد بسیارمحبوب! کلامی را که من به تو می‌گویم فهم کن وبر پایهای خود بایست زیرا که الان نزد تو فرستاده شده‌ام.» و چون این کلام را به من گفت لرزان بایستادم.۱۱
12 Sai ya ci gaba da cewa, “Kada ka ji tsoro, Daniyel. Gama tun daga ran da ka fara sa zuciya ga neman ganewa, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Allahnka, an ji addu’arka, amsar addu’arka ce ta kawo ni.
و مرا گفت: «ای دانیال مترس زیرا از روزاول که دل خود را بر آن نهادی که بفهمی و به حضور خدای خود تواضع نمایی سخنان تومستجاب گردید و من به‌سبب سخنانت آمده‌ام.۱۲
13 Amma mai mulkin masarautar Farisa ya tsare ni har kwana ashirin da ɗaya. Sai da Mika’ilu, ɗaya daga cikin manya shugabanni, ya zo ya taimake ni, saboda an tsare ni a can tare da sarkin Farisa.
اما رئیس مملکت فارس بیست و یک روز بامن مقاومت نمود و میکائیل که یکی از روسای اولین است به اعانت من آمد و من در آنجا نزدپادشاهان فارس ماندم.۱۳
14 Yanzu na zo domin in bayyana maka abin da zai faru da mutanenka nan gaba, gama wahayin ya shafi lokacin da bai riga ya zo ba ne.”
و من آمدم تا تو را ازآنچه در ایام آخر بر قوم تو واقع خواهد شداطلاع دهم زیرا که این‌رویا برای ایام طویل است.»۱۴
15 Yayinda yake faɗin mini haka, sai na sunkuyar da kaina ƙasa shiru, ba magana.
و چون اینگونه سخنان را به من گفته بود به روی خود بر زمین افتاده، گنگ شدم.۱۵
16 Sai wani wanda ya yi kama da mutum ya taɓa leɓunana, na kuma buɗe bakina sai na fara magana. Na ce wa wannan da yake tsaye a gabana, “Na cika da azaba saboda wannan wahayi, ranka yă daɗe, ina kuma neman taimako.
که ناگاه کسی به شبیه بنی آدم لبهایم را لمس نمود و من دهان خود را گشوده، متکلم شدم و به آن کسی‌که پیش من ایستاده بود گفتم: «ای آقایم از این‌رویادرد شدیدی مرا در‌گرفته است و دیگر هیچ قوت نداشتم.۱۶
17 Yaya ni bawanka zan iya magana da kai, ranka yă daɗe? Ƙarfina ya ƙare kuma ina numfashi da ƙyar.”
پس چگونه بنده آقایم بتواند با آقایم گفتگو نماید و حال آنکه از آن وقت هیچ قوت درمن برقرار نبوده، بلکه نفس هم در من باقی نمانده است.»۱۷
18 Har yanzu wannan wanda yana kama da mutum ya taɓa ni ya kuma ba ni ƙarfi.
پس شبیه انسانی بار دیگر مرا لمس نموده، تقویت داد،۱۸
19 Ya kuma ce, “Kada ka ji tsoro, ya kai mutumin da ake fahariya, salama a gare ka! Ka ƙarfafa yanzu; ka yi ƙarfin hali.” Sa’ad da ya yi magana da ni, sai na samu ƙarfi na ce, “Ka yi magana ranka yă daɗe, tun da yake ka sa na sami ƙarfi.”
و گفت: «ای مرد بسیارمحبوب مترس! سلام بر تو باد و دلیر و قوی باش!» چون این را به من گفت تقویت یافتم و گفتم: «ای آقایم بگو زیرا که مرا قوت دادی.»۱۹
20 Sai ya ce mini, “Ka san abin da ya kawo ni gare ka? Ba da jimawa ba zan koma in yi yaƙi da mai mulkin Farisa, kuma idan na tafi, mai mulkin Hellenawa zai taso;
پس گفت: «آیا می‌دانی که سبب آمدن من نزد توچیست؟ و الان برمی گردم تا با رئیس فارس جنگ نمایم و به مجرد بیرون رفتنم اینک رئیس یونان خواهد آمد.۲۰
21 amma da farko zan faɗa maka abin da aka rubuta a cikin Littafin Gaskiya (Babu wanda ya taimake ni yaƙi da waɗannan sai dai Mika’ilu, sarkinku.
لیکن تو را از آنچه در کتاب حق مرقوم است اطلاع خواهم داد و کسی غیر ازرئیس شما میکائیل نیست که مرا به ضد اینها مددکند.۲۱

< Daniyel 10 >