< Daniyel 10 >
1 A shekara ta uku ta Sairus sarkin Farisa, sai aka ba wa Daniyel (wanda ake kira Belteshazar) wahayi. Saƙon kuwa gaskiya ce wadda take tattare da babban yaƙi. Fahimtar saƙon ya zo masa a cikin wahayi.
During the third year that Cyrus was the king of Persia, I Daniel, [who had been given the] name Belteshazzar, received [another] message [from God]. The message was true, but it was very difficult for me to understand it. But [later] I understood the message because of the vision that I had seen.
2 A wannan lokaci ni Daniyel na yi makoki har na sati uku.
At that time I had been sad for three weeks [about what had happened to Jerusalem].
3 Ban ci abinci mai kyau ba; ba nama ko ruwa inabin da ya shiga bakina; kuma ba na amfani da man shafawa gaba ɗaya har sai da sati nan uku suka wuce.
I did not eat any tasty food or any meat or drink any wine. I did not even put any perfumed oil on my [face or hair] for those three weeks.
4 A rana ta ashirin da huɗu ga watan farko, a sa’ad da nake tsaye a bakin babban kogi, Tigris,
[When those three weeks ended, ] on April 23, [my companions and] I were standing on the bank of the great Tigris River.
5 na ɗaga kaina na duba sai ga wani mutum tsaye sanye da rigar lilin, ya yi ɗamara da zinariya zalla daga Ufaz kewaye da ƙugunsa.
I looked up and saw someone there who was wearing fine white/linen clothes and a belt [made of] pure gold.
6 Jikinsa kamar lu’ulu’u yake, fuskarsa kuma kamar walƙiya, idanunsa kamar harshen wuta, hannuwansa da ƙafafunsa kamar gogaggiyar tagulla, muryarsa kuma kamar amon babban taron jama’a.
His body [shone] like a precious beryl stone. His face was as [bright as] a flash of lightning. His eyes [were/shone] like flaming torches. His arms and legs [shone] like polished bronze. And his voice was [very loud], like the roar of a huge crowd.
7 Ni, Daniyel, kaɗai ne na ga wahayin; mutanen da suke tare da ni ba su gani ba, amma wata irin babbar razana ta auko musu har suka gudu suka ɓuya.
I, Daniel, was the only one who saw this vision. The men who were with me did not see anything, but [they sensed that someone was there, and they] became terrified. They ran away and hid themselves.
8 Sai aka bar ni ni kaɗai, ina juyayi wannan babban wahayi, ba ni da sauran ƙarfi, fuskata ta yamutse kuma ba ni da sauran ƙarfi.
So I was left there by myself, looking at this very unusual vision. I had no strength left. My face became very pale, with the result that no one would have recognized me.
9 Sai na ji yana magana, da ina sauraronsa, sai na shiga barci mai nauyi, na kuwa fāɗi rubda ciki.
I saw a man there, and when I heard him speak, I fell to the ground. I (fainted/became unconscious), [and I lay there] with my face on the ground.
10 Sai hannu ya taɓa ni ya sa makyarkyata a hannuna da ƙafafuna.
Suddenly someone’s hand took hold of me and lifted me, with the result that I was on my hands and knees, [but I was still] trembling.
11 Sai ya ce, “Daniyel, kai ne wanda ake ƙauna sosai, ka yi lura da kyau game da kalmomin da zan yi maka magana a kansu, ka tashi yanzu, gama an aiko ni a gare ka.” Sa’ad da ya faɗa mini haka, sai na tashi a tsaye ina rawan jiki.
The man said to me, “Daniel, [God] loves you very much. Stand up and listen to what I am going to say to you, because [God] sent me to you.” When he said that, I stood up, [but I was still] trembling.
12 Sai ya ci gaba da cewa, “Kada ka ji tsoro, Daniyel. Gama tun daga ran da ka fara sa zuciya ga neman ganewa, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Allahnka, an ji addu’arka, amsar addu’arka ce ta kawo ni.
Then he said to me, “Daniel, do not be afraid. God has heard what you have prayed ever since the first day that you determined to humble yourself in order to understand [the vision]. I have come to you because of what you prayed.
13 Amma mai mulkin masarautar Farisa ya tsare ni har kwana ashirin da ɗaya. Sai da Mika’ilu, ɗaya daga cikin manya shugabanni, ya zo ya taimake ni, saboda an tsare ni a can tare da sarkin Farisa.
The [evil spirit who] rules the kingdom of Persia resisted/hindered me for 21 days, but Michael, who is one of God’s chief angels, came to help me. I left him there in Persia [to resist] that evil spirit who rules there.
14 Yanzu na zo domin in bayyana maka abin da zai faru da mutanenka nan gaba, gama wahayin ya shafi lokacin da bai riga ya zo ba ne.”
I have come here to enable you to understand what will happen to the Israeli people in the future. [Do not forget that] the vision [that you saw] is about [things that will happen in] the distant future, [not about things that will happen very soon].”
15 Yayinda yake faɗin mini haka, sai na sunkuyar da kaina ƙasa shiru, ba magana.
While he was saying that, I stared at the ground and was unable to say anything [because I was very afraid].
16 Sai wani wanda ya yi kama da mutum ya taɓa leɓunana, na kuma buɗe bakina sai na fara magana. Na ce wa wannan da yake tsaye a gabana, “Na cika da azaba saboda wannan wahayi, ranka yă daɗe, ina kuma neman taimako.
Suddenly [the angel], who resembled a human, touched my lips. Then [I was able to speak, and] I said to him, “Sir, because [I have seen] this vision, I have become very weak, with the result that I cannot stop trembling.
17 Yaya ni bawanka zan iya magana da kai, ranka yă daɗe? Ƙarfina ya ƙare kuma ina numfashi da ƙyar.”
I am not able [RHQ] to talk to you, my master. I have no strength left, and it is very difficult for me to breathe.”
18 Har yanzu wannan wanda yana kama da mutum ya taɓa ni ya kuma ba ni ƙarfi.
But he took hold of me again, and enabled me to become stronger again.
19 Ya kuma ce, “Kada ka ji tsoro, ya kai mutumin da ake fahariya, salama a gare ka! Ka ƙarfafa yanzu; ka yi ƙarfin hali.” Sa’ad da ya yi magana da ni, sai na samu ƙarfi na ce, “Ka yi magana ranka yă daɗe, tun da yake ka sa na sami ƙarfi.”
He said to me, “You human, God loves you very much. [So] do not be afraid. I desire/want things to go well for you and that you will be encouraged.” When he had said that, I felt even stronger, and I said, “Sir, tell me [what you want to tell me]. You have enabled me to feel stronger.”
20 Sai ya ce mini, “Ka san abin da ya kawo ni gare ka? Ba da jimawa ba zan koma in yi yaƙi da mai mulkin Farisa, kuma idan na tafi, mai mulkin Hellenawa zai taso;
Then he said, “(Do you know why I came to you?/I will tell you why I came to you.) [RHQ] It is to reveal to you what is written in the book which reveals/contains God’s truth. But now I must return to fight against [the evil spirit] who rules the kingdom of Persia. After I have defeated him, [the evil angel] who guards Greece will appear [and I must defeat him]. Michael, who guards you [Israeli people], will help me, but there is no one else to help me.”
21 amma da farko zan faɗa maka abin da aka rubuta a cikin Littafin Gaskiya (Babu wanda ya taimake ni yaƙi da waɗannan sai dai Mika’ilu, sarkinku.