< Daniyel 1 >

1 A Shekara ta uku ta mulki Yehohiyakim sarkin Yahuda, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zo Urushalima ya kuma yi mata ƙawanya.
I Judas konge Jojakims tredje regjeringsår drog Nebukadnesar, kongen i Babel, til Jerusalem og kringsatte det.
2 Sai Ubangiji ya bashe Yehohiyakim sarkin Yahuda a hannunsa, tare da waɗansu kayayyakin haikalin Allah. Ya ɗauki waɗannan kayan zuwa cikin haikalin allahnsa a Babilon cikin ma’ajin gidan allahnsa.
Og Herren gav Judas konge Jojakim i hans hånd, og likeledes en del av karene i Guds hus, og han førte dem til Sinears land, til sin guds hus - han lot karene sette inn i sin guds skattkammer.
3 Sa’an nan sarkin ya umarci Ashfenaz, shugaban fadarsa yă kawo waɗansu daga cikin Isra’ilawan da suka fito daga gidan sarauta da kuma na fitattun mutane.
Og kongen sa til Aspenas, sin øverste hoffmann, at han skulde ta med sig nogen av Israels barn, både av kongeætten og av de fornemste,
4 Matasa maza waɗanda ba su da wata naƙasa kuma kyawawa, hazikai ta kowace hanyar koyo, sanannu, masu saurin fahimtar abu, da kuma waɗanda suka cancanci su yi aiki a fadar sarki. Zai koya musu harshen Babiloniyawa da kuma littattafansu.
unge gutter som var uten lyte og fagre å se til, og med evne til å tilegne sig all slags visdom og vinne kunnskap og bli kyndige i videnskap, og som var dyktige til å tjene i kongens palass, og at de skulde oplæres i kaldeernes skrift og tungemål.
5 Sarki kuma ya sa a ba su abinci da ruwan inabi kowace rana daga cikin abincin sarki. Za a koyar da su har shekaru uku, bayan haka kuma su shiga yin wa sarki hidima.
Og kongen fastsatte hvad de hver dag skulde ha av kongens kostelige mat og av den vin han drakk, og bød at de skulde opdras i tre år, og når disse år var omme, skulde de bli kongens tjenere.
6 Daga cikin waɗannan da aka zaɓa akwai waɗansu daga Yahuda, Daniyel, Hananiya, Mishayel da kuma Azariya.
Blandt dem var av Judas barn Daniel, Hananja, Misael og Asarja.
7 Sai sarkin fada ya raɗa musu sababbin sunaye, ga Daniyel ya raɗa masa Belteshazar; ga Hananiya ya raɗa masa Shadrak; ga Mishayel ya raɗa masa Meshak; ga Azariya kuma ya raɗa masa Abednego.
Og den øverste hoffmann gav dem nye navn: Daniel kalte han Beltsasar og Hananja Sadrak og Misael Mesak og Asarja Abed-Nego.
8 Amma Daniyel ya ƙudura a zuciyarsa ba zai ƙazantar da kansa da abinci da ruwan inabin sarki ba, sai ya tambayi sarkin fada don a ba shi izinin kada yă ƙazantar da kansa ta wannan hanya.
Men Daniel satte sig fore at han ikke vilde gjøre sig uren med kongens kostelige mat og med den vin han drakk, og han bad den øverste hoffmann om at han måtte være fri for således å gjøre sig uren.
9 Sai Allah ya sa sarkin fada ya nuna masa tagomashi ya kuma ƙaunaci Daniyel,
Og Gud lot Daniel finne velvilje og barmhjertighet hos den øverste hoffmann.
10 amma sai sarkin fada ya ce wa Daniyel, “Ina jin tsoron ranka yă daɗe, sarkina wanda ya sa a ba ku abinci da ruwan inabi. Me zai sa yă ga kuna ramewa fiye da sauran samari, tsaranku? Sarki zai sa a fille mini kai saboda ku.”
Og den øverste hoffmann sa til Daniel: Jeg er redd for at min herre kongen, som har fastsatt hvad I skal ete og drikke, vil synes at eders ansikter ser dårligere ut enn de gutters som er på eders alder, og at I således skal føre skyld over mitt hode hos kongen.
11 Sai Daniyel ya ce wa mai gadi wanda sarkin fada ya sa yă kula da Daniyel, Hananiya, Mishayel da Azariya,
Da sa Daniel til kjellermesteren, som den øverste hoffmann hadde satt over Daniel, Hananja, Misael og Asarja:
12 “Ina roƙonka ka gwada bayinka kwana goma. Kada ka ba mu kome sai kayan lambu mu ci da kuma baƙin ruwa mu sha.
Kjære, prøv det med dine tjenere i ti dager og la dem gi oss grønnsaker å ete og vann å drikke,
13 Sa’an nan sai ka dubi fuskokinmu da na sauran samarin da suke ci daga abincin sarki; sa’an nan ka yi da bayinka bisa ga abin da ka gani.”
så kan du siden ta vårt utseende i øiesyn, og likeså de gutters utseende som eter kongens kostelige mat, og gjør så med dine tjenere efter det du da ser!
14 Sai ya amince da haka ya kuma gwada su har kwana goma.
Og han gjorde som de ønsket, og prøvde det med dem i ti dager.
15 A ƙarshen kwana goma sai aka ga fuskokinsu suna sheƙi, sun kuma yi ƙiba fiye da samarin da suke cin abinci irin na sarki.
Og da de ti dager var omme, viste det sig at de var fagrere å se til og i bedre hold enn alle de gutter som hadde ett av kongens kostelige mat.
16 Sai mai gadinsu ya janye abinci da ruwan inabi irin na sarki, ya ci gaba da ba su kayan lambu.
Da lot kjellermesteren deres kostelige mat bære bort, og likeså den vin de skulde drikke, og gav dem grønnsaker.
17 Ga samarin nan guda huɗu Allah ya ba su sani da ganewar dukan irin littattafai da kuma koyarwa. Daniyel kuma ya iya gane wahayi da kowane irin mafarki.
Og Gud gav disse fire gutter kunnskap og forstand på all slags skrift og visdom, og Daniel skjønte sig på alle slags syner og drømmer.
18 A ƙarshen lokacin da sarki ya sa da za a kawo su ciki, sai sarkin fada ya gabatar da su ga Nebukadnezzar.
Da den tid kongen hadde fastsatt, var til ende, og de skulde fremstilles for ham, førte den øverste hoffmann dem inn for Nebukadnesar.
19 Sarki kuwa ya yi magana da su, sai ya gano cewa babu wani kamar Daniyel, Hananiya, Mishayel da kuma Azariya; don haka sai suka shiga yi wa sarki hidima.
Og kongen talte med dem, og det fantes ikke blandt alle de unge gutter nogen som kunde måle sig med Daniel, Hananja, Misael og Asarja; så blev de da kongens tjenere.
20 A dukan al’amuran hikima da na fahimta wanda sarki ya tambaye su, ya tarar sun fi dukan masu sihiri da bokaye waɗanda suke cikin mulkinsa sau goma.
Og i enhver sak som krevde visdom og forstand, og som kongen spurte dem om, fant han at de ti ganger overgikk alle de tegnsutleggere og åndemanere som fantes i hele hans rike.
21 Daniyel kuwa ya kasance a nan har shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus.
Og Daniel blev der like til kong Kyros' første år.

< Daniyel 1 >