< Daniyel 1 >

1 A Shekara ta uku ta mulki Yehohiyakim sarkin Yahuda, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zo Urushalima ya kuma yi mata ƙawanya.
In the third year of the reign of Jehoiakim, the king of Judah, came Nebuchadnezzar, the king of Babylon, against Jerusalem, and besieged it.
2 Sai Ubangiji ya bashe Yehohiyakim sarkin Yahuda a hannunsa, tare da waɗansu kayayyakin haikalin Allah. Ya ɗauki waɗannan kayan zuwa cikin haikalin allahnsa a Babilon cikin ma’ajin gidan allahnsa.
And the Lord gave Jehoiakim, the king of Judah, into his hand, with part of the vessels of the house of God; and he carried them into the land of Shinar, to the house of his god; and he brought the vessels into the treasure-house of his god.
3 Sa’an nan sarkin ya umarci Ashfenaz, shugaban fadarsa yă kawo waɗansu daga cikin Isra’ilawan da suka fito daga gidan sarauta da kuma na fitattun mutane.
And the king commanded Ashpenaz, the master of his eunuchs, that he should bring certain of the sons of Israel of the king's race, and of the princes,
4 Matasa maza waɗanda ba su da wata naƙasa kuma kyawawa, hazikai ta kowace hanyar koyo, sanannu, masu saurin fahimtar abu, da kuma waɗanda suka cancanci su yi aiki a fadar sarki. Zai koya musu harshen Babiloniyawa da kuma littattafansu.
youths in whom was no blemish, and well favored, and skilful in all wisdom, and having knowledge and intelligence and strength, to stand as servants in the king's palace, and be taught the writing and the language of the Chaldaeans.
5 Sarki kuma ya sa a ba su abinci da ruwan inabi kowace rana daga cikin abincin sarki. Za a koyar da su har shekaru uku, bayan haka kuma su shiga yin wa sarki hidima.
And the king appointed them a daily provision of the king's food, and of the wine which he drank; so nourishing them three years, that at the end thereof they might stand as servants before the king.
6 Daga cikin waɗannan da aka zaɓa akwai waɗansu daga Yahuda, Daniyel, Hananiya, Mishayel da kuma Azariya.
Now among these were, of the sons of Judah, Daniel, Hananiah, Mishael, and Azariah.
7 Sai sarkin fada ya raɗa musu sababbin sunaye, ga Daniyel ya raɗa masa Belteshazar; ga Hananiya ya raɗa masa Shadrak; ga Mishayel ya raɗa masa Meshak; ga Azariya kuma ya raɗa masa Abednego.
And the prince of the eunuchs gave them other names. To Daniel he gave the name of Belteshazzar; and to Hananiah, of Shadrach; and to Mishael, of Meshach; and to Azariah, of Abednego.
8 Amma Daniyel ya ƙudura a zuciyarsa ba zai ƙazantar da kansa da abinci da ruwan inabin sarki ba, sai ya tambayi sarkin fada don a ba shi izinin kada yă ƙazantar da kansa ta wannan hanya.
But Daniel purposed in his heart that he would not defile himself with the portion of the king's meat, nor with the wine which he drank; therefore he requested of the prince of the eunuchs that he might not defile himself.
9 Sai Allah ya sa sarkin fada ya nuna masa tagomashi ya kuma ƙaunaci Daniyel,
And God gave Daniel favor and kindness from the prince of the eunuchs.
10 amma sai sarkin fada ya ce wa Daniyel, “Ina jin tsoron ranka yă daɗe, sarkina wanda ya sa a ba ku abinci da ruwan inabi. Me zai sa yă ga kuna ramewa fiye da sauran samari, tsaranku? Sarki zai sa a fille mini kai saboda ku.”
And the prince of the eunuchs said to Daniel, I fear my lord the king, who hath appointed your meat and your drink; for he might see your faces in worse condition than the youths of your age; then shall ye make me endanger my head to the king.
11 Sai Daniyel ya ce wa mai gadi wanda sarkin fada ya sa yă kula da Daniyel, Hananiya, Mishayel da Azariya,
Then said Daniel to the steward whom the prince of the eunuchs had set over Daniel, Hananiah, Mishael, and Azariah,
12 “Ina roƙonka ka gwada bayinka kwana goma. Kada ka ba mu kome sai kayan lambu mu ci da kuma baƙin ruwa mu sha.
Try thy servants ten days, and let them give us pulse to eat, and water to drink.
13 Sa’an nan sai ka dubi fuskokinmu da na sauran samarin da suke ci daga abincin sarki; sa’an nan ka yi da bayinka bisa ga abin da ka gani.”
Then let our countenances be looked upon before thee, and the countenances of the youths that eat of the portion of the king's meat; and as thou seest, deal with thy servants.
14 Sai ya amince da haka ya kuma gwada su har kwana goma.
And he consented to them in this matter, and tried them ten days.
15 A ƙarshen kwana goma sai aka ga fuskokinsu suna sheƙi, sun kuma yi ƙiba fiye da samarin da suke cin abinci irin na sarki.
And at the end of ten days their countenances appeared fairer and fatter in flesh than all the youths who ate the portion of the king's meat.
16 Sai mai gadinsu ya janye abinci da ruwan inabi irin na sarki, ya ci gaba da ba su kayan lambu.
So the steward took away the portion of their meat, and the wine which they should drink, and gave them pulse.
17 Ga samarin nan guda huɗu Allah ya ba su sani da ganewar dukan irin littattafai da kuma koyarwa. Daniyel kuma ya iya gane wahayi da kowane irin mafarki.
And God gave these four youths knowledge and skill in all learning and wisdom; and Daniel had understanding in all visions and dreams.
18 A ƙarshen lokacin da sarki ya sa da za a kawo su ciki, sai sarkin fada ya gabatar da su ga Nebukadnezzar.
And at the end of the days, when the king had commanded him to bring them before him, then the prince of the eunuchs brought them in before Nebuchadnezzar.
19 Sarki kuwa ya yi magana da su, sai ya gano cewa babu wani kamar Daniyel, Hananiya, Mishayel da kuma Azariya; don haka sai suka shiga yi wa sarki hidima.
And the king conversed with them; and among them all was found none like Daniel, Hananiah, Mishael, and Azariah. Therefore they stood as servants before the king.
20 A dukan al’amuran hikima da na fahimta wanda sarki ya tambaye su, ya tarar sun fi dukan masu sihiri da bokaye waɗanda suke cikin mulkinsa sau goma.
And in all matters of wisdom and understanding concerning which the king inquired of them, he found them ten times better than all the scribes and magicians that were in all his realm.
21 Daniyel kuwa ya kasance a nan har shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus.
And Daniel lived even to the first year of Cyrus the king.

< Daniyel 1 >