< Kolossiyawa 4 >
1 Masu bayi, ku riƙe bayinku da kyau da kuma daidai, domin kun san cewa ku ma kuna da Ubangiji a sama.
Los señores traten con justicia y equidad a sus esclavos. Sepan que también ustedes tienen [al] Señor en [el] cielo.
2 Ku nace da yin addu’a, kuna zaman tsaro da kuma godiya.
Perseveren en la conversación con Dios y velen en ella con acción de gracias.
3 Ku kuma yi mana addu’a, mu ma, don Allah yă buɗe ƙofa saboda saƙonmu, don mu iya yin shelar asirin Kiristi, wanda saboda shi nake cikin sarƙoƙi.
Al mismo tiempo hablen con Dios también por nosotros, para que Dios nos abra una puerta de proclamación a fin de anunciar el misterio de Cristo, por el cual fui encadenado,
4 Ku yi addu’a yadda zan yi shelarsa, yadda ya kamata.
para que lo proclame como debo hacerlo.
5 Ku zama masu hikima a yadda kuke ma’amala da waɗanda suke ba masu bi ba; ku kuma yi amfani da kowane zarafi.
Vivan con sabiduría en relación con los de afuera y aprovechen bien el tiempo.
6 Bari maganarku kullum ta zama da ladabi da kuma daɗin ji, domin ku san amsar da ta dace ku ba wa kowa.
La palabra de ustedes sea siempre con gracia, sazonada con sal para que sepan cómo les conviene responder.
7 Tikikus shi ne ƙaunataccen ɗan’uwan nan, wanda ya yi aiki da aminci a hidimar Ubangiji tare da mu, zai kuwa faɗa muku dukan labari game da ni.
Todas las cosas con respecto a mí se las informará Tíquico, el hermano amado, fiel ministro y consiervo en [el] Señor,
8 Ina aikansa shi a gare ku musamman domin ku san yadda muke, yă kuma ƙarfafa muku zuciya.
a quien les envié para que conozcan nuestra situación y consuele sus corazones.
9 Yana zuwa tare da Onesimus, ƙaunatacce da kuma amintaccen mai bin nan, wanda yake ɗaya daga cikinku. Za su gaya muku dukan abin da yake faruwa a nan.
[También les envié] a Onésimo, el fiel y amado hermano, quien es de ustedes. [Ellos] les informarán todas las cosas de aquí.
10 Aristarkus yana a kurkuku tare da ni. Yana gaishe ku, haka ma Markus, wanda kakansa ɗaya ne da Barnabas. (Shi ne na riga na yi magana a kansa, na ce muku in ya zo, ku karɓe shi hannu biyu-biyu.)
Aristarco, mi compañero de prisión, los saluda y Marcos, el primo de Bernabé, con respecto a quien les dí mandamientos. Si los visita, recíbanlo.
11 Yesu, wannan da muke kira Yustus, shi ma yana gaisuwa. Waɗannan ne kaɗai Yahudawa masu bi a cikin abokan aikina saboda mulkin Allah. Sun kuma zama da taimako a gare ni.
[También los saluda] Jesús, el llamado Justo. Ellos son colaboradores conmigo en el reino de Dios y me consolaron. Son judíos.
12 Efafaras naku, mai hidimar Kiristi Yesu, yana gaisuwa. Kullum yana addu’a dominku sosai, don ku san cikakken abin da Allah yake so ku yi don kuma ku yi shi cikakke.
Los saluda Epafras, quien es de ustedes y esclavo de Cristo, y se esfuerza siempre por ustedes en toda [la] voluntad de Dios.
13 Na tabbatar muku, cewa yana aiki ƙwarai dominku da kuma domin waɗanda suke a Lawodiseya da Hiyerafolis.
Porque doy testimonio de que él tiene mucha aflicción por ustedes, y por los que están en Laodicea y en Hierápolis.
14 Luka ƙaunataccen likitan nan, da kuma Demas suna gaishe ku.
Los saluda Lucas, el médico amado, y Demas.
15 Ku miƙa gaisuwata ga’yan’uwan da suke a Lawodiseya, musamman ga Nimfa da kuma ikkilisiyar da take taru a gidanta.
Saluden a los hermanos que están en Laodicea, a Ninfa y a la iglesia de la casa de ella.
16 Bayan an karanta muku wannan wasiƙa, ku tabbata an karanta ta kuma a ikkilisiyar Lawodiseyawa; ku ma ku karanta wasiƙar da ta zo daga Lawodiseya.
Cuando esta epístola sea leída por ustedes, permitan que también se lea en la iglesia de Laodicea, y que ustedes también lean la de Laodicea.
17 Ku faɗa wa Arkiffus yă tabbata ya ƙarasa aikin da ya karɓa cikin Ubangiji.
Digan a Arquipo: Considera el ministerio que recibiste del Señor, para que lo cumplas.
18 Ni Bulus ne nake rubuta muku wannan gaisuwa da hannuna. Ku tuna da sarƙoƙina. Alherin Allah yă kasance tare da ku.
El saludo de mi mano, de Pablo. Recuerden mis cadenas. La gracia sea con ustedes.