< Kolossiyawa 3 >

1 Da yake an tashe ku tare da Kiristi, sai ku sa zukatanku a kan abubuwan da suke sama, inda Kiristi yake zaune a hannun dama na Allah.
Kui te koos Kristusega olete üles äratatud, siis taotlege seda, mis on ülal, kus Kristus istub Jumala paremal käel.
2 Ku sa hankulanku a kan abubuwan sama, ba kan abubuwan duniya ba.
Mõtelge sellele, mis on ülal, mitte sellele, mis on maa peal,
3 Gama kun mutu, ranku yanzu kuwa yana ɓoye tare da Kiristi a cikin Allah.
sest teie olete surnud ja teie elu on Kristusega varjul Jumalas.
4 Sa’ad da Kiristi, wanda shi ne ranku, ya bayyana, ku ma za ku bayyana tare da shi cikin ɗaukaka.
Kui Kristus, kes on teie elu, saab avalikuks, siis saate ka teie koos temaga avalikuks auhiilguses.
5 Saboda haka, sai ku fid da duk wani abin da yake kawo sha’awa a zukatanku, fasikanci, ƙazanta, sha’awa, muguwar sha’awa, da kuma kwaɗayi wanda shi ma bautar gumaka ne.
Seepärast surmake nüüd endas kõik maine: hoorus, räpasus, kired, kurjad himud ja ahnus, mis on ebajumalateenistus;
6 Gama fushin Allah zai sauko a kan masu aikata waɗannan.
nende pärast tuleb Jumala viha.
7 Dā kun yi waɗannan abubuwa, sa’ad da rayuwar tana cikin duniya mai wannan hali.
Teiegi käisite varem nendes, kui te sellist elu elasite.
8 Amma yanzu dole ku raba kanku da dukan ire-iren abubuwan nan. Ku daina fushi, ku daina ƙiyayya da ƙeta. Ku bar ɓatan suna da kuma ƙazamar magana daga leɓunanku.
Nüüd aga jätke maha kõik see: viha, raev, õelus, laim, räpased sõnad oma huultelt.
9 Kada ku yi wa juna ƙarya, da yake kun tuɓe tsohon halinku tare da ayyukansa
Ärge valetage üksteisele, sest te olete vana inimese tema harjumustega lahti riietanud
10 kun ɗauki sabon halin nan da ake sabuntawa ga sani, bisa ga kamannin Mahaliccinsa.
ja rõivastunud uue inimesega, keda uuendatakse õigesti tunnetama oma Looja näo kohaselt.
11 A wannan sabuwar rayuwa babu bambanci ko kai mutumin Al’ummai ne ko mutumin Yahuda, mai kaciya ne ko marar kaciya, baƙo, baƙauye, bawa ne ko’yantacce, gama Kiristi shi ne kome, kuma yana cikin kome.
Nii pole enam kreeklast ega juuti, ümberlõigatut ega ümberlõikamatut, võõramaalast ega sküüti, ei orja ega vaba, vaid kõik ja kõikides on Kristus.
12 Da yake Allah ya mai da ku zaɓaɓɓu, tsarkaka, ƙaunatattu, sai ku dinga jin tausayin juna, kuna yin alheri, kuna nuna tawali’u da sauƙinkai da jimrewa.
Rõivastuge siis nagu sobib Jumala valitud pühale ja armastatud rahvale: kaastunde, lahkuse, alandlikkuse, leebuse ja pika meelega.
13 Ku riƙa yin haƙuri da juna kuna kuma gafarta wa juna duk wani laifin da wani ya yi muku. Ku gafarta kamar yadda Ubangiji ya gafarce ku.
Sallige üksteist ja andke üksteisele andeks, kui kellelgi on midagi teise vastu. Nagu Issand teile on andeks andnud, andke ka teie!
14 Fiye da waɗannan duka, ku yi ƙaunar juna, gama ƙauna ce take haɗa kome gaba ɗaya.
Aga kõige selle üle olgu armastus, mis teid täiuslikus ühtsuses kokku seob.
15 Ku bar salamar Kiristi tă yi mulki a zukatanku, da yake a matsayin gaɓoɓin jiki ɗaya an kira ku ga salama. Ku zama masu godiya.
Ja teie südameis valitsegu Kristuse rahu, sest selleks te olete ühe ihuna kutsutud. Ja olge tänulikud!
16 Ku bar maganar Kiristi ta zauna a cikinku a yalwace yayinda kuke koya, kuna kuma yi wa juna gargaɗi da dukan hikima, da kuma yayinda kuke waƙoƙin zabura, waƙoƙi da waƙoƙin ruhaniya tare da godiya a zukatanku ga Allah.
Kristuse sõna elagu rikkalikult teie sees! Kogu tarkuses õpetage ja manitsege üksteist psalmide, hümnide ja Vaimus antud lauludega, lauldes tänuliku südamega Jumalale!
17 Kuma ko mene ne kuke yi, ko cikin magana ko cikin ayyuka, ku yi shi duka a cikin sunan Ubangiji Yesu, kuna yin godiya ga Allah Uba ta wurinsa.
Ja kõik, mida iganes te teete sõna või teoga, seda tehke Issanda Jeesuse nimel, tänades Isa Jumalat tema kaudu.
18 Mata, ku yi biyayya ga mazanku, yadda ya dace cikin Ubangiji.
Naised, alistuge meestele, nagu on kohane Issandas!
19 Maza, ku ƙaunaci matanku kada ku nuna musu hali marar tausayi.
Mehed, armastage oma naisi ja ärge tehke nende elu kibedaks!
20 ’Ya’ya, ku yi biyayya ga iyayenku cikin kome, gama wannan yakan gamshi Ubangiji.
Lapsed, olge kuulekad oma vanematele igas asjas, sest see meeldib Issandale!
21 Ubanni, kada ku matsa wa yaranku lamba, don kada su fid da zuciya.
Isad, ärge kohelge oma lapsi liiga karmilt, et nad ei kaotaks julgust!
22 Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku na duniya cikin kome; kada ku yi aikin ganin ido kamar masu neman yabon mutane, sai dai ku yi aiki tsakaninku da Allah, kamar masu tsoron Ubangiji.
Orjad, kuuletuge oma maistele isandatele kõiges, mitte ainult nende silme all nagu need, kes püüavad inimestele meeldida, vaid siira südamega, kartes Issandat.
23 Kome kuke yi, ku yi shi da dukan zuciyarku, sai ka ce ga Ubangiji kuke yi, ba ga mutum ba.
Mida te iganes teete, tehke kogu südamest, nii nagu Issandale ja mitte nagu inimestele,
24 Kun san cewa zai ba ku gādo a matsayin ladanku. Ubangiji Kiristi ne fa kuke bauta wa.
sest te teate, et saate Issandalt tasuks pärandi. Teenige Issandat Kristust!
25 Duk wanda ya yi laifi, za a sāka masa don laifinsa, babu sonkai.
Aga sellele, kes teeb ülekohut, tasutakse tema ülekohtu järgi, ega tehta vahet isikute vahel.

< Kolossiyawa 3 >