< Kolossiyawa 3 >

1 Da yake an tashe ku tare da Kiristi, sai ku sa zukatanku a kan abubuwan da suke sama, inda Kiristi yake zaune a hannun dama na Allah.
If, then, ye were raised with the Christ, the things above seek ye, where the Christ is, on the right hand of God seated,
2 Ku sa hankulanku a kan abubuwan sama, ba kan abubuwan duniya ba.
the things above mind ye, not the things upon the earth,
3 Gama kun mutu, ranku yanzu kuwa yana ɓoye tare da Kiristi a cikin Allah.
for ye did die, and your life hath been hid with the Christ in God;
4 Sa’ad da Kiristi, wanda shi ne ranku, ya bayyana, ku ma za ku bayyana tare da shi cikin ɗaukaka.
when the Christ — our life — may be manifested, then also we with him shall be manifested in glory.
5 Saboda haka, sai ku fid da duk wani abin da yake kawo sha’awa a zukatanku, fasikanci, ƙazanta, sha’awa, muguwar sha’awa, da kuma kwaɗayi wanda shi ma bautar gumaka ne.
Put to death, then, your members that [are] upon the earth — whoredom, uncleanness, passion, evil desire, and the covetousness, which is idolatry —
6 Gama fushin Allah zai sauko a kan masu aikata waɗannan.
because of which things cometh the anger of God upon the sons of the disobedience,
7 Dā kun yi waɗannan abubuwa, sa’ad da rayuwar tana cikin duniya mai wannan hali.
in which also ye — ye did walk once, when ye lived in them;
8 Amma yanzu dole ku raba kanku da dukan ire-iren abubuwan nan. Ku daina fushi, ku daina ƙiyayya da ƙeta. Ku bar ɓatan suna da kuma ƙazamar magana daga leɓunanku.
but now put off, even ye, the whole — anger, wrath, malice, evil-speaking, filthy talking — out of your mouth.
9 Kada ku yi wa juna ƙarya, da yake kun tuɓe tsohon halinku tare da ayyukansa
Lie not one to another, having put off the old man with his practices,
10 kun ɗauki sabon halin nan da ake sabuntawa ga sani, bisa ga kamannin Mahaliccinsa.
and having put on the new, which is renewed in regard to knowledge, after the image of Him who did create him;
11 A wannan sabuwar rayuwa babu bambanci ko kai mutumin Al’ummai ne ko mutumin Yahuda, mai kaciya ne ko marar kaciya, baƙo, baƙauye, bawa ne ko’yantacce, gama Kiristi shi ne kome, kuma yana cikin kome.
where there is not Greek and Jew, circumcision and uncircumcision, foreigner, Scythian, servant, freeman — but the all and in all — Christ.
12 Da yake Allah ya mai da ku zaɓaɓɓu, tsarkaka, ƙaunatattu, sai ku dinga jin tausayin juna, kuna yin alheri, kuna nuna tawali’u da sauƙinkai da jimrewa.
Put on, therefore, as choice ones of God, holy and beloved, bowels of mercies, kindness, humble-mindedness, meekness, long-suffering,
13 Ku riƙa yin haƙuri da juna kuna kuma gafarta wa juna duk wani laifin da wani ya yi muku. Ku gafarta kamar yadda Ubangiji ya gafarce ku.
forbearing one another, and forgiving each other, if any one with any one may have a quarrel, as also the Christ did forgive you — so also ye;
14 Fiye da waɗannan duka, ku yi ƙaunar juna, gama ƙauna ce take haɗa kome gaba ɗaya.
and above all these things, [have] love, which is a bond of the perfection,
15 Ku bar salamar Kiristi tă yi mulki a zukatanku, da yake a matsayin gaɓoɓin jiki ɗaya an kira ku ga salama. Ku zama masu godiya.
and let the peace of God rule in your hearts, to which also ye were called in one body, and become thankful.
16 Ku bar maganar Kiristi ta zauna a cikinku a yalwace yayinda kuke koya, kuna kuma yi wa juna gargaɗi da dukan hikima, da kuma yayinda kuke waƙoƙin zabura, waƙoƙi da waƙoƙin ruhaniya tare da godiya a zukatanku ga Allah.
Let the word of Christ dwell in you richly, in all wisdom, teaching and admonishing each other, in psalms, and hymns, and spiritual songs, in grace singing in your hearts to the Lord;
17 Kuma ko mene ne kuke yi, ko cikin magana ko cikin ayyuka, ku yi shi duka a cikin sunan Ubangiji Yesu, kuna yin godiya ga Allah Uba ta wurinsa.
and all, whatever ye may do in word or in work, [do] all things in the name of the Lord Jesus — giving thanks to the God and Father, through him.
18 Mata, ku yi biyayya ga mazanku, yadda ya dace cikin Ubangiji.
The wives! be subject to your own husbands, as is fit in the Lord;
19 Maza, ku ƙaunaci matanku kada ku nuna musu hali marar tausayi.
the husbands! love your wives, and be not bitter with them;
20 ’Ya’ya, ku yi biyayya ga iyayenku cikin kome, gama wannan yakan gamshi Ubangiji.
the children! obey the parents in all things, for this is well-pleasing to the Lord;
21 Ubanni, kada ku matsa wa yaranku lamba, don kada su fid da zuciya.
the fathers! vex not your children, lest they be discouraged.
22 Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku na duniya cikin kome; kada ku yi aikin ganin ido kamar masu neman yabon mutane, sai dai ku yi aiki tsakaninku da Allah, kamar masu tsoron Ubangiji.
The servants! obey in all things those who are masters according to the flesh, not in eye-service as men-pleasers, but in simplicity of heart, fearing God;
23 Kome kuke yi, ku yi shi da dukan zuciyarku, sai ka ce ga Ubangiji kuke yi, ba ga mutum ba.
and all, whatever ye may do — out of soul work — as to the Lord, and not to men,
24 Kun san cewa zai ba ku gādo a matsayin ladanku. Ubangiji Kiristi ne fa kuke bauta wa.
having known that from the Lord ye shall receive the recompense of the inheritance — for the Lord Christ ye serve;
25 Duk wanda ya yi laifi, za a sāka masa don laifinsa, babu sonkai.
and he who is doing unrighteously shall receive what he did unrighteously, and there is no acceptance of persons.

< Kolossiyawa 3 >