< Kolossiyawa 3 >
1 Da yake an tashe ku tare da Kiristi, sai ku sa zukatanku a kan abubuwan da suke sama, inda Kiristi yake zaune a hannun dama na Allah.
If then ye were raised together with Christ, seek the things that are above, where Christ is, seated on the right hand of God.
2 Ku sa hankulanku a kan abubuwan sama, ba kan abubuwan duniya ba.
Set your mind on the things that are above, not on the things that are upon the earth.
3 Gama kun mutu, ranku yanzu kuwa yana ɓoye tare da Kiristi a cikin Allah.
For ye died, and your life is hid with Christ in God.
4 Sa’ad da Kiristi, wanda shi ne ranku, ya bayyana, ku ma za ku bayyana tare da shi cikin ɗaukaka.
When Christ, [who is] our life, shall be manifested, then shall ye also with him be manifested in glory.
5 Saboda haka, sai ku fid da duk wani abin da yake kawo sha’awa a zukatanku, fasikanci, ƙazanta, sha’awa, muguwar sha’awa, da kuma kwaɗayi wanda shi ma bautar gumaka ne.
Mortify therefore your members which are upon the earth; fornication, uncleanness, passion, evil desire, and covetousness, the which is idolatry;
6 Gama fushin Allah zai sauko a kan masu aikata waɗannan.
for which things’ sake cometh the wrath of God upon the sons of disobedience;
7 Dā kun yi waɗannan abubuwa, sa’ad da rayuwar tana cikin duniya mai wannan hali.
in the which ye also walked aforetime, when ye lived in these things.
8 Amma yanzu dole ku raba kanku da dukan ire-iren abubuwan nan. Ku daina fushi, ku daina ƙiyayya da ƙeta. Ku bar ɓatan suna da kuma ƙazamar magana daga leɓunanku.
But now put ye also away all these; anger, wrath, malice, railing, shameful speaking out of your mouth:
9 Kada ku yi wa juna ƙarya, da yake kun tuɓe tsohon halinku tare da ayyukansa
lie not one to another; seeing that ye have put off the old man with his doings,
10 kun ɗauki sabon halin nan da ake sabuntawa ga sani, bisa ga kamannin Mahaliccinsa.
and have put on the new man, which is being renewed unto knowledge after the image of him that created him:
11 A wannan sabuwar rayuwa babu bambanci ko kai mutumin Al’ummai ne ko mutumin Yahuda, mai kaciya ne ko marar kaciya, baƙo, baƙauye, bawa ne ko’yantacce, gama Kiristi shi ne kome, kuma yana cikin kome.
where there cannot be Greek and Jew, circumcision and uncircumcision, barbarian, Scythian, bondman, freeman: but Christ is all, and in all.
12 Da yake Allah ya mai da ku zaɓaɓɓu, tsarkaka, ƙaunatattu, sai ku dinga jin tausayin juna, kuna yin alheri, kuna nuna tawali’u da sauƙinkai da jimrewa.
Put on therefore, as God’s elect, holy and beloved, a heart of compassion, kindness, humility, meekness, longsuffering;
13 Ku riƙa yin haƙuri da juna kuna kuma gafarta wa juna duk wani laifin da wani ya yi muku. Ku gafarta kamar yadda Ubangiji ya gafarce ku.
forbearing one another, and forgiving each other, if any man have a complaint against any; even as the Lord forgave you, so also do ye:
14 Fiye da waɗannan duka, ku yi ƙaunar juna, gama ƙauna ce take haɗa kome gaba ɗaya.
and above all these things [put on] love, which is the bond of perfectness.
15 Ku bar salamar Kiristi tă yi mulki a zukatanku, da yake a matsayin gaɓoɓin jiki ɗaya an kira ku ga salama. Ku zama masu godiya.
And let the peace of Christ rule in your hearts, to the which also ye were called in one body; and be ye thankful.
16 Ku bar maganar Kiristi ta zauna a cikinku a yalwace yayinda kuke koya, kuna kuma yi wa juna gargaɗi da dukan hikima, da kuma yayinda kuke waƙoƙin zabura, waƙoƙi da waƙoƙin ruhaniya tare da godiya a zukatanku ga Allah.
Let the word of Christ dwell in you richly in all wisdom; teaching and admonishing one another with psalms [and] hymns [and] spiritual songs, singing with grace in your hearts unto God.
17 Kuma ko mene ne kuke yi, ko cikin magana ko cikin ayyuka, ku yi shi duka a cikin sunan Ubangiji Yesu, kuna yin godiya ga Allah Uba ta wurinsa.
And whatsoever ye do, in word or in deed, [do] all in the name of the Lord Jesus, giving thanks to God the Father through him.
18 Mata, ku yi biyayya ga mazanku, yadda ya dace cikin Ubangiji.
Wives, be in subjection to your husbands, as is fitting in the Lord.
19 Maza, ku ƙaunaci matanku kada ku nuna musu hali marar tausayi.
Husbands, love your wives, and be not bitter against them.
20 ’Ya’ya, ku yi biyayya ga iyayenku cikin kome, gama wannan yakan gamshi Ubangiji.
Children, obey your parents in all things, for this is well-pleasing in the Lord.
21 Ubanni, kada ku matsa wa yaranku lamba, don kada su fid da zuciya.
Fathers, provoke not your children, that they be not discouraged.
22 Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku na duniya cikin kome; kada ku yi aikin ganin ido kamar masu neman yabon mutane, sai dai ku yi aiki tsakaninku da Allah, kamar masu tsoron Ubangiji.
Servants, obey in all things them that are your masters according to the flesh; not with eyeservice, as men-pleasers, but in singleness of heart, fearing the Lord:
23 Kome kuke yi, ku yi shi da dukan zuciyarku, sai ka ce ga Ubangiji kuke yi, ba ga mutum ba.
whatsoever ye do, work heartily, as unto the Lord, and not unto men;
24 Kun san cewa zai ba ku gādo a matsayin ladanku. Ubangiji Kiristi ne fa kuke bauta wa.
knowing that from the Lord ye shall receive the recompense of the inheritance: ye serve the Lord Christ.
25 Duk wanda ya yi laifi, za a sāka masa don laifinsa, babu sonkai.
For he that doeth wrong shall receive again for the wrong that he hath done: and there is no respect of persons.