< Kolossiyawa 2 >
1 Ina so ku san irin famar da nake yi saboda ku da kuma waɗanda suke a Lawodiseya, da kuma saboda dukan waɗanda ba su taɓa ganina ido da ido ba.
Nangmih neh Laodicea kah rhoek ham thingthuelnah mat ka khueh he khaw, hlang boeih loh pumsa kah ka maelhmai he a hmuh pawt te khaw nangmih ming sak ka ngaih.
2 Manufata ita ce a ƙarfafa su su kuma zama ɗaya a cikin ƙauna. Ina so su kasance da cikakken ƙarfin hali domin suna da cikakken fahimtar asirin Allah, wato, Kiristi kansa,
Te daengah ni amih kah thinko te a hloep vetih, Khrih neh Pathen kah olhuep mingnah ham lungnah neh ngaikhueknah khuehtawn cungkuem dongah yakmingnah neh n'cului eh.
3 a cikinsa ne aka ɓoye dukkan dukiya ta hikima da ta sani.
Amah khuiah cueihnah khohrhang neh mingnah olhuep cungkuem te om.
4 Ina faɗa muku wannan ne don kada wani yă ruɗe ku da daɗin baki.
He he ka thui daengah ni nangmih te yoeknah neh n'yoek pawt eh.
5 Gama ko da yake ba na nan tare da ku a cikin jiki, ina tunaninku kullum, ina kuma farin ciki da gani kuna rayuwa yadda ya kamata, kuna kuma dāgewarku a kan bangaskiyarku a cikin Kiristi.
Pumsa neh lakhla mai sitoe cakhaw mueihla nen tah nangmih taengah ka om. Omngaih neh aka tueng khaw nangmih kah khuetnetnah, Khrih dongah khangmainah, nangmih kah tangnah pawn ni.
6 To, da yake kun karɓi Kiristi Yesu a matsayin Ubangiji, sai ku ci gaba da rayuwa a cikinsa,
Te dongah Boeipa Jesuh Khrih te na doe uh vanbangla amah dongah pongpa uh.
7 ku tsaya daram ku kuma ginu a cikinsa, ku sami ƙarfafawa a cikin bangaskiya kamar yadda aka koya muku, kuna kuma cike da godiya.
Amah dongah yung aka pael tih aka khueng loh n'thuituen vanbangla tangnah dongah cak uh lah. Uemonah neh baetawt uh lah.
8 Ku lura kada wani yă ruɗe ku da ilimin banza da wofi. Wannan koyarwa ta mutane ce kawai. Ta fito daga ikokin wannan duniya ne ba daga Kiristi ba.
Poeksoemnah lamloh a payawk tih hlang kah singyoe bangla hmilhmaknah neh a tlonglai pakhat khaw na om pawt ham ngaithuen uh. Diklai kah a niing la om uh tih Khrih kah la a om uh moenih.
9 Gama a cikin Kiristi cikin jiki dukkan cikar Allahntaka take tabbata,
Amah dongah Pathen coengnah pumrho kah a soepnah la boeih om.
10 an kuma mai da ku cikakku a cikin Kiristi, wanda yake shi ne kai a kan kowane iko da kuma hukuma.
Te dongah amah dongah ni a soep la na om uh. Anih tah boeilu neh saithainah boeih kah a lu la om.
11 A cikinsa ne kuma aka yi muku kaciya, ba kuwa yin mutum ba, amma wadda Kiristi ya yi muku, ta wurin tuɓe halinku na mutuntaka.
Te phoeiah Khrih kah yahvinrhetnah dongah pumsa pum kah duulnah neh amah dongah kutsai mueh yahvinrhetnah neh yahvin na rhet uh.
12 Da yake an binne ku tare da shi cikin baftisma haka kuma aka tashe ku tare da shi ta wurin bangaskiyarku a cikin ikon Allah, wanda ya tashe shi daga matattu.
Baptisma dongah amah neh m'vuei uh tih duek lamkah anih aka thoh Pathen bibi dongkah tangnah rhangneh amah neh na thoo uh coeng.
13 Kun zama matattu saboda ku masu zunubi ne kuma saboda halin zunubanku aka ware. Sa’an nan Allah ya sa kuka rayu tare da Kiristi. Ya gafarta mana dukan zunubanmu.
Nangmih he aka duek tholhdalhnah neh na pumsa kah pumdul dongah na om uh. Tedae nangmih te amah neh n'thoh tih tholhdalhnah cungkuem khuikah mamih he khodawk a ngai.
14 Ya soke rubutacciyar doka tare da ƙa’idodinta, wadda take gāba da mu, take kuma hamayya da mu; ya kuma kawar da ta, ya kafe ta a kan gicciye.
Mamih taengkah kut neh a daek oltloek, mamih ham kingkalh la aka om te a huih coeng tih a khoe tih thinglam ah a hen.
15 Bayan ya ƙwace makaman ikoki da hukumomi, ya kunyata su a sarari, ya ci nasara a bisansu ta wurin gicciye.
Boeilu rhoek te a khah tih saithainah te sayalh la a yan. Te nen te amih a na coeng.
16 Saboda haka kada ku bar wani yă shari’anta ku a kan abin da kuke ci ko sha, ko bisa ga abin da ya shafi wani bikin addini, ko Bikin Sabon Wata ko na ranar Asabbaci.
Nangmih te khaw caak cak neh an ok dongah khaw, khotue vaengah khaw, hlasae neh Sabbath ah pakhat long khaw n'coel tangloeng boel saeh.
17 Waɗannan su ne hoton abubuwan da za su zo; amma Kiristi ne ainihinsu.
Te rhoek te aka lo ham koi kah mueihlip ni. Tedae Khrih pum ni kungpuei.
18 Kada ku yarda wani yă ɓata ku, cewa shi wani abu ne don yă ga wahayi. Irin mutumin nan yakan nuna ƙasƙancin kai na ƙarya, yă kuma ce yana yi wa mala’iku sujada. Irin mutumin nan yana kumbura kansa ba dalili, sai son zuciya irin na halin mutuntaka.
Nangmih te tlayaenah dongah aka hmae neh puencawn rhoek kah a bawknah loh n'hloo sak boel saeh. Anih loh tuektuek a hmuh te a pumsa kah lungbuei neh a hoeihae la a hoemdawk puei.
19 Ya yanke dangantaka da Kiristi wanda yake kai, wanda ta gare shi ne dukan jiki yake a haɗe, yake tsaye ta wurin taimakon gaɓoɓi da jijiyoyi, yana kuma girma kamar yadda Allah yake sa yă yi girma.
Lu te a tuuk moenih. Anih lamloh rhuhcong neh tharhui thanal neh pum tom te a duel. Te vaengah Pathen kah rhoengnah dongla cului uh tih rhoeng van.
20 Kun mutu tare da Kiristi. Yanzu ƙa’idodin wannan duniya ba su da iko a kanku. Don me kuke zama har yanzu kamar ku nasu ne? Kuna biyayya da umarnansu cewa,
Diklai kah a niing lamloh Khrih neh na duek uh atah balae tih Diklai ah aka cuep lalah la na hing uh.
21 “Kada ka kama! Kada ka ɗanɗana! Kada ka taɓa”?
Taek boeh, ten boeh, ben boeh,
22 Irin waɗannan dokoki suna magana a kan abubuwan da ba sa daɗewa. Su ayyukan mutane ne, sun kuma fito daga koyarwar mutane.
hlang kah olpaek neh thuituennah bangla a hnonah te a hmawnnah ham ni boeih a om te.
23 Yin biyayya da irin waɗannan ƙa’idodi za su yi kamar su ne abu mafi kyau da za a yi. Sukan yi kamar suna sa a ƙaunaci Allah sosai a kuma kasance da sauƙinkai a kuma kasance da kamunkai. Amma ba su da wani iko a kan sha’awace-sha’awacenmu.
Te rhoek te poeklawt thothueng, tlayaenah neh pum phaepnah dongah olka hong neh cueihnah aka khueh la om uh. Pumsa kah huengaihnah tah pakhat khaw a phu om pawh.