< Kolossiyawa 1 >

1 Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, da kuma daga Timoti ɗan’uwanmu,
Surat ini berasal dari Paulus, rasul dari Kristus Yesus sesuai dengan kehendak Allah, dan dari saudara seiman kami, Timotius,
2 Zuwa ga tsarkaka da kuma amintattun’yan’uwa cikin Kiristi da suke a Kolossi. Alheri da salama daga Allah Ubanmu, su kasance tare da ku.
kepada seluruh mempercayai orang Kristen di kota Kolose, semoga damai sejahtera dan kebaikan Allah Bapa kita turun atas kalian.
3 Kullum muna gode wa Allah, Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, sa’ad da muke addu’a dominku.
Kami selalu bersyukur kepada Allah Bapa dari Tuhan Kristus Yesus ketika kami mendoakan kalian.
4 Gama mun ji labarin bangaskiyarku a cikin Yesu Kiristi da kuma ƙaunar da kuke yi saboda dukan tsarkaka.
Kami mendengar tentang betapa kalian sungguh percaya kepada Kristus Yesus dan kasih kalian kepada semua orang percaya
5 Kuna yin haka ne kuwa domin abin da kuke bege yana a ajiye a sama. Kun riga kun ji game da wannan bege sa’ad da kuka gaskata saƙon nan na gaskiya wanda shi ne bisharar
karena harapan yang disiapkan untukmu di surga. Kalian sudah mendengar tentang kabar baik ini, pesan tentang kebenaran ini
6 da ta zo muku. Ko’ina a duniya wannan bishara tana yi ta haihuwa tana kuma girma, kamar yadda take yi a cikinku tun daga ranar da kuka ji ta kuka kuma fahimci alherin Allah cikin dukan gaskiyarta.
yang menghampiri kalian, seperti halnya Kabar Baik itu tersebar ke seluruh dunia, menyebar dengan luas dan membuat banyak orang menjadi percaya kepada Yesus. Hal yang sama sudah terjadi pada kalian juga, sejak kalian mendengar tentang Kabar Baik itu dan menyadari sifat dari kebaikan hati Allah yang sebenarnya.
7 Kun koyi wannan gaskiya daga wurin Efafaras, ƙaunataccen abokin hidimarmu, wanda yake amintacce mai hidimar Kiristi a madadinmu,
Epafras, teman dan rekan kerja kami yang terkasih, yang merupakan seorang pekerja Kristus yang bisa dipercaya sebagai wakil kami, yang mengajarkan kalian tentang hal ini.
8 wanda kuma ya faɗa mana ƙaunar da kuke yi cikin Ruhu.
Dia juga menerangkan kepada kami tentang kasih kalian yang berasal dari Roh.
9 Shi ya sa tun daga ranar da muka sami labarin, ba mu fasa yin addu’a dominku ba. Kullum muna roƙon Allah yă sa ku san kome da yake so ku yi, domin ku sami hikima ta Ruhu, ku kuma sami ganewar kome duka.
Oleh karena itu kami terus berdoa bagi kalian sejak kami mendengar tentang kalian, meminta agar Allah memberikan kepada kalian pemahaman akan tugas yang Dia ingin agar kalian lakukan dan memberikan kepada kalian setiap kebijasanaan dan pemahaman rohani.
10 Ta haka za ku yi rayuwa wadda ta dace da Ubangiji, ku kuma gamshe shi a ta kowace hanya, kuna yin aiki mai kyau ta kowace hanya, kuna kuma yin girma cikin sanin Allah.
Dengan demikian kalian akan menjalani hidup kalian dengan cara yang tepat sebagai wakil Tuhan dan menyenangkan Dia, memberikan segala hasil yang baik dan mendapatkan pengenalan tentang Allah lebih baik lagi.
11 Allah yă ƙarfafa ku da dukan iko bisa ga ɗaukakar ƙarfinsa domin ku kasance da jimrewa sosai da kuma haƙuri, cikin farin ciki
Kiranya kalian menjadi kuat oleh karena kuasa-Nya yang ajaib, penuh kesabaran dan daya tahan.
12 kuna gode wa Uba, wanda ya sa kuka cancanci ku sami rabo a gādon tsarkaka a cikin mulkin haske.
Kiranya kalian memuji Allah Bapa dengan penuh sukacita, yang menjadikan kita pewaris bersama umat Allah yang hidup dengan cara yang hidup dalam terang.
13 Gama ya riga ya cece mu daga mulkin duhu ya kuma kawo mu cikin mulkin Ɗan da yake ƙauna,
Dia menyelamatkan kita dari kuasa kegelapan dan membawa kita masuk ke dalam kerajaan Anak yang dikasihi-Nya,
14 wanda ta wurinsa muka sami fansa da kuma gafarar zunubai.
yang melalui Dia kita sudah dibebaskan dan dosa kita diampuni.
15 Kiristi shi ne surar da ake gani na Allah wanda ba a iya gani, ɗan fari a kan dukan halitta.
Anak adalah gambar yang terlihat dari Allah yang tidak terlihat. Dia ada sebelum semua ciptaan,
16 Ta wurinsa aka halicci dukan abu, abubuwan da suke cikin sama da abubuwan da suke a duniya, waɗanda ake gani, da waɗanda ba a gani, ko kursiyoyi ko ikoki ko masu mulki ko hukumomi; an halicci dukan abu ta wurinsa da kuma dominsa ne.
sebab segala sesuatu diciptakan melalui Dia — di dalam surga dan di atas bumi, yang bisa kita lihat dengan mata dan yang tidak bisa kita lihat dengan mata, kerajaan, para penguasa, para pemimpin dan pemerintahan — segala sesuatu di dunia ini diciptakan melalui Dia dan untuk Dia.
17 Ya kasance kafin dukan abu, kuma a cikinsa ne dukan abubuwa suke a harhaɗe.
Dia ada sebelum segalanya, dan Dia menyatukan segalanya.
18 Shi ne kuma kan ikkilisiya, wadda take jikinsa. Shi ne mafari da kuma na farko da ya tashi daga matattu, domin a cikin kowane abu yă zama mafifici.
Dia juga adalah kepala dari semua orang yang percaya kepada-Nya. Dia adalah yang awal, yang pertama dan teratas dari mereka yang dihidupkan kembali dari kematian, dengan demikian Dia menjadi yang paling utama di atas segalanya.
19 Gama Allah ya ji daɗi yă sa dukan cikarsa ta kasance a cikin Kiristi,
Allah senang memiliki sifat penuh-Nya yang hidup di dalam diri-Nya,
20 ta wurin Kiristi ne ya komar da kome zuwa ga kansa. Ya kawo salama ga abubuwan da suke ƙasa da abubuwan da suke sama, ta wurin jinin Kiristi da ya zubar a kan gicciye.
dan melalui Dia, Allah membawa kembali semua yang ada di alam semesta ini kembali kepada diri-Nya sendiri, karena Dia membuat perdamaian melalui darah salib-Nya, dan melalui Dia mendamaikan semua di bumi dan di surga.
21 A dā kuna a ware da Allah, kuka kuma zama abokan gāba a cikin tunaninku saboda mugun halinku.
Kalian pernah terasing dari Allah, musuh dalam cara berpikir dan cara kalian bertindak,
22 Amma Ɗansa ya zama mutum ya kuma mutu. Saboda haka Allah ya yi sulhu da ku, yanzu kuwa ya bar ku ku tsaya a gabansa da tsarki, marasa aibi, da kuma marasa abin zargi.
tetapi sekarang Dia telah mendamaikan kalian melalui tubuh manusia-Nya yang sekarat, membawa kalian ke hadirat-Nya di mana kalian berdiri suci, murni, dan tak bercacat.
23 Sai ku ci gaba cikin bangaskiyarku, kuna tsaye a kafe kuma tsayayyu, ba tare da gusawa daga begen da kuka ji daga bishara ba. Wannan ita ce bisharar da kuka ji wadda aka yi shelarta ga kowace halittar da take ƙarƙashin sama, wadda kuma ni Bulus, na zama mai hidimarta.
Tetapi rasa percaya kalian kepadanya haruslah terus seteguh batu karang dan tidak tergoyahkan. Janganlah keluar dari harapan Kabar Baik yang sudah kalian dengar, Kabar Baik yang sudah diberitakan ke seluruh dunia — itulah pekerjaan yang saya, Paulus, sudah lakukan.
24 Yanzu, ina farin ciki saboda wuyar da nake sha dominku, don ta wurin wuyan nan zan cika abin da ya rage na wuyar da Kiristi ya sha saboda jikinsa, wato, ikkilisiya.
Saya bersukacita jika harus menderita demi kalian, jika itu artinya yang terjadi padaku secara jasmani saya menjadi bagian dari penderitaan Kristus yang terus menerus Dia alami demi tubuh-Nya, jemaat-Nya.
25 Na zama mai hidimar ikkilisiya bisa ga aikin nan da Allah ya ba ni amana saboda ku, domin in sanar da maganar Allah sosai.
Saya melayani jemaat mengikuti arahan yang Allah berikan tentang kalian, untuk memberitakan tentang firman Allah secara lengkap kepada kalian.
26 Wannan magana da nake gaya muku asiri ne da yake a ɓoye tun zamanai masu yawa, wanda yanzu aka bayyana ga tsarkaka. (aiōn g165)
Inilah rahasia yang tersembunyi selama berabad-abad dari sejak permulaan dunia, tetapi sekarang telah diwahyukan kepada umat Allah. (aiōn g165)
27 Su ne Allah ya so yă sanar da yadda irin yalwar ɗaukakar asirin nan take a cikin al’ummai, asirin nan kuwa shi ne Kiristi a cikinku, begen ɗaukakar da za a bayyana.
Allah ingin memperkenalkan diri kepada mereka tentang kekayaan dan kemuliaan dari rahasia ini kepada bangsa-bangsa bukan Yahudi: Kristus yang tinggal di dalam kalian adalah harapan yang mulia!
28 Saboda haka ko’ina muka tafi, muna shela, muna gargaɗi, muna kuma koyar da kowa da dukan hikima, don mu miƙa kowa cikakke a cikin Kiristi.
Itu sebabnya kami menceritakan kepada setiap orang tentang Kristus, mengajar dan mengarahkan mereka dengan cara terbaik yang kami tahu agar kami bisa membawa setiap orang ke hadapan Allah sampai mereka dewasa secara rohani di dalam Kristus.
29 Don haka ne ina fama, ina kuma ƙoƙari da duk ƙarfin nan da Kiristi ya ba ni.
Inilah yang saya kerjakan juga, berusaha keras dengan mengandalkan kekuatan yang Yesus berikan yang bekerja dengan penuh kuasa di dalam saya.

< Kolossiyawa 1 >