< Kolossiyawa 1 >
1 Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, da kuma daga Timoti ɗan’uwanmu,
From Paul, an apostle of Christ Jesus, by the will of God, and from Timothy, also a follower of the Lord.
2 Zuwa ga tsarkaka da kuma amintattun’yan’uwa cikin Kiristi da suke a Kolossi. Alheri da salama daga Allah Ubanmu, su kasance tare da ku.
To Christ’s people at Colossae – the followers who are faithful to him: May God, our Father, bless you and give you peace.
3 Kullum muna gode wa Allah, Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, sa’ad da muke addu’a dominku.
Whenever we pray we never fail to thank God, the Father of our Lord Jesus Christ, for you,
4 Gama mun ji labarin bangaskiyarku a cikin Yesu Kiristi da kuma ƙaunar da kuke yi saboda dukan tsarkaka.
now that we have heard of your faith in Christ Jesus and of the love that you have for all his people,
5 Kuna yin haka ne kuwa domin abin da kuke bege yana a ajiye a sama. Kun riga kun ji game da wannan bege sa’ad da kuka gaskata saƙon nan na gaskiya wanda shi ne bisharar
because of the hope which is kept safe for you in heaven. Of this hope you heard long ago in the true message of the good news which reached you,
6 da ta zo muku. Ko’ina a duniya wannan bishara tana yi ta haihuwa tana kuma girma, kamar yadda take yi a cikinku tun daga ranar da kuka ji ta kuka kuma fahimci alherin Allah cikin dukan gaskiyarta.
bearing fruit and growing, as it does, through all the world, just as it did among you from the very day that you heard of God’s loving kindness, and understood what that loving kindness really is.
7 Kun koyi wannan gaskiya daga wurin Efafaras, ƙaunataccen abokin hidimarmu, wanda yake amintacce mai hidimar Kiristi a madadinmu,
It is just what you learned from Epaphras, our dear fellow servant, who, as a minister of the Christ, faithfully represents us,
8 wanda kuma ya faɗa mana ƙaunar da kuke yi cikin Ruhu.
and who told us of the love with which the Spirit has inspired you.
9 Shi ya sa tun daga ranar da muka sami labarin, ba mu fasa yin addu’a dominku ba. Kullum muna roƙon Allah yă sa ku san kome da yake so ku yi, domin ku sami hikima ta Ruhu, ku kuma sami ganewar kome duka.
And therefore we, from the very day that we heard this, have never ceased praying for you, or asking that you may be filled with the knowledge of the will of God, which comes through all true spiritual wisdom and insight.
10 Ta haka za ku yi rayuwa wadda ta dace da Ubangiji, ku kuma gamshe shi a ta kowace hanya, kuna yin aiki mai kyau ta kowace hanya, kuna kuma yin girma cikin sanin Allah.
Then you will live lives worthy of the Master, and so please God in every way. Your lives will be fruitful in every kind of good action, and grow into a fuller knowledge of God;
11 Allah yă ƙarfafa ku da dukan iko bisa ga ɗaukakar ƙarfinsa domin ku kasance da jimrewa sosai da kuma haƙuri, cikin farin ciki
you will be made strong at all points with a strength worthy of the power manifested in his glory – strong to endure with patience, and even with gladness, whatever may happen to you;
12 kuna gode wa Uba, wanda ya sa kuka cancanci ku sami rabo a gādon tsarkaka a cikin mulkin haske.
and you will give thanks to the Father who made you fit to share the lot which awaits Christ’s people in the realms of light.
13 Gama ya riga ya cece mu daga mulkin duhu ya kuma kawo mu cikin mulkin Ɗan da yake ƙauna,
For God has rescued us from the tyranny of darkness, and has removed us into the kingdom of his Son, who is the embodiment of his love,
14 wanda ta wurinsa muka sami fansa da kuma gafarar zunubai.
and through whom we have found deliverance in the forgiveness of our sins.
15 Kiristi shi ne surar da ake gani na Allah wanda ba a iya gani, ɗan fari a kan dukan halitta.
For Christ is the incarnation of the invisible God – firstborn and head of all creation;
16 Ta wurinsa aka halicci dukan abu, abubuwan da suke cikin sama da abubuwan da suke a duniya, waɗanda ake gani, da waɗanda ba a gani, ko kursiyoyi ko ikoki ko masu mulki ko hukumomi; an halicci dukan abu ta wurinsa da kuma dominsa ne.
for in him was created all that is in heaven and on earth, the visible and the invisible – angels and archangels and all the powers of heaven.
17 Ya kasance kafin dukan abu, kuma a cikinsa ne dukan abubuwa suke a harhaɗe.
All has been created through him and for him. He was before all things, and all things unite in him;
18 Shi ne kuma kan ikkilisiya, wadda take jikinsa. Shi ne mafari da kuma na farko da ya tashi daga matattu, domin a cikin kowane abu yă zama mafifici.
and he is the head of the church, which is his body. The firstborn from the dead, he is to the church the source of its life, that he, in all things, may stand first.
19 Gama Allah ya ji daɗi yă sa dukan cikarsa ta kasance a cikin Kiristi,
For it pleased the Father that in him the divine nature in all its fulness should live,
20 ta wurin Kiristi ne ya komar da kome zuwa ga kansa. Ya kawo salama ga abubuwan da suke ƙasa da abubuwan da suke sama, ta wurin jinin Kiristi da ya zubar a kan gicciye.
and through him to reconcile all things to himself (making peace by the shedding of Christ’s blood offered on the cross) – whether on earth or in heaven.
21 A dā kuna a ware da Allah, kuka kuma zama abokan gāba a cikin tunaninku saboda mugun halinku.
And it pleased God that you, once estranged from him and hostile towards him in your thoughts, intent only on wickedness –
22 Amma Ɗansa ya zama mutum ya kuma mutu. Saboda haka Allah ya yi sulhu da ku, yanzu kuwa ya bar ku ku tsaya a gabansa da tsarki, marasa aibi, da kuma marasa abin zargi.
but now he has reconciled you to himself by the sacrifice of Christ’s earthly body in death – it has pleased God that you should stand in his presence holy, pure, and blameless,
23 Sai ku ci gaba cikin bangaskiyarku, kuna tsaye a kafe kuma tsayayyu, ba tare da gusawa daga begen da kuka ji daga bishara ba. Wannan ita ce bisharar da kuka ji wadda aka yi shelarta ga kowace halittar da take ƙarƙashin sama, wadda kuma ni Bulus, na zama mai hidimarta.
if only you remain true to your faith, firm and immovable, never abandoning the hope held out in the good news to which you listened, which has been proclaimed among all created things under heaven, and of which I, Paul, was made an assistant.
24 Yanzu, ina farin ciki saboda wuyar da nake sha dominku, don ta wurin wuyan nan zan cika abin da ya rage na wuyar da Kiristi ya sha saboda jikinsa, wato, ikkilisiya.
Now at last I can rejoice in my sufferings on your behalf, and in my own person I supplement the afflictions endured by the Christ, for the sake of his body, the church;
25 Na zama mai hidimar ikkilisiya bisa ga aikin nan da Allah ya ba ni amana saboda ku, domin in sanar da maganar Allah sosai.
of which I myself became a minister in virtue of the office with which God entrusted me for your benefit, to declare the message of God in all its fulness –
26 Wannan magana da nake gaya muku asiri ne da yake a ɓoye tun zamanai masu yawa, wanda yanzu aka bayyana ga tsarkaka. (aiōn )
that truth which has been hidden from former ages and generations. But now it has been revealed to God’s people, (aiōn )
27 Su ne Allah ya so yă sanar da yadda irin yalwar ɗaukakar asirin nan take a cikin al’ummai, asirin nan kuwa shi ne Kiristi a cikinku, begen ɗaukakar da za a bayyana.
to whom it was his pleasure to make known the surpassing glory of that hidden truth when proclaimed among the Gentiles – ‘Christ among you! Your hope of glory!’
28 Saboda haka ko’ina muka tafi, muna shela, muna gargaɗi, muna kuma koyar da kowa da dukan hikima, don mu miƙa kowa cikakke a cikin Kiristi.
This is the Christ whom we proclaim, warning everyone, and instructing everyone, with all the wisdom that we possess, in the hope of bringing everyone into God’s presence perfected by union with Christ.
29 Don haka ne ina fama, ina kuma ƙoƙari da duk ƙarfin nan da Kiristi ya ba ni.
It is for that I toil, struggling with all the energy which he inspires and which works powerfully within me.