< Amos 1 >
1 Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
The wordis of Amos ben these, that was in the schepherdis thingis of Thecue, whiche he siy on Israel, in the daies of Osie, king of Juda, and in the daies of Jeroboam, sone of Joas, kyng of Israel, bifor twei yeeris of the erthe mouynge.
2 Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
And he seide, The Lord schal rore fro Sion, and schal yyue his vois fro Jerusalem; and the faire thingis of schepherdis mourenyden, and the cop of Carmele was maad drie.
3 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
The Lord seith these thingis, On thre grete trespassis of Damask, and on foure, I shal not conuerte it, for it threischide Galaad in irun waynes.
4 zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
And Y schal sende fier in to the hous of Asael, and it schal deuoure the housis of Benadab.
5 Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
And Y schal al to-breke the barre of Damask, and Y schal leese a dwellere fro the feeld of idol, and hym that holdith the ceptre fro the hous of lust and of letcherie; and the puple of Sirie schal be translatid to Sirenen, seith the Lord.
6 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
The Lord seith these thingis, On thre grete trespassis of Gasa, and on foure, Y schal not conuerte it, for it translatide perfit caitifte, to close that togidere in Idumee.
7 Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
And Y schal sende fier in to the wal of Gasa, and it schal deuoure the housis therof.
8 Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And Y schal leese the dwelleris of Azotus, and hym that holdith the ceptre of Ascalon; and Y schal turne myn hond on Accaron, and the remenauntis of Filisteis schulen perische, seith the Lord God.
9 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
The Lord God seith these thingis, On thre grete trespassis of Tire, and on foure, Y schal not conuerte it, for thei closiden togidere perfit caitifte in Idumee, and hadde not mynde on the boond of pees of britheren.
10 zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
And Y schal sende fier in to the wal of Tire, and it schal deuoure the housis therof.
11 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
The Lord seith these thingis, On thre grete trespassis of Edom, and on foure, Y schal not conuerte it, for it pursuede bi swerd his brother, and defoulide the merci of hym, and helde ferthere his woodnesse, and kepte his indignacioun `til in to the ende.
12 Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
Y schal sende fier in to Theman, and it schal deuoure the housis of Bosra.
13 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
The Lord seith these thingis, On thre grete trespassis of the sones of Amon, and on foure, Y schal not conuerte hym, for he karf the wymmen with childe of Galaad, for to alarge his terme.
14 Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
And Y schal kyndle fier in the wal of Rabbe, and it schal deuoure the housis therof, in yellyng in the dai of batel, and in whirlwynd in the dai of mouyng togidere.
15 Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.
And Melchon schal go in to caitifte, he and hise princes togidere, seith the Lord.