< Amos 1 >
1 Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
These are the things concerning Israel that Amos, one of the shepherds in Tekoa, received in revelation. He received these things in the days of Uzziah king of Judah, and also in the days of Jeroboam son of Joash king of Israel, two years before the earthquake.
2 Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
He said, “Yahweh will roar from Zion; he will raise his voice from Jerusalem. The pastures of the shepherds will dry up; the top of Carmel will wither.”
3 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
This is what Yahweh says: “For three sins of Damascus, even for four, I will not turn away punishment, because they threshed Gilead with instruments of iron.
4 zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
I will send a fire into the house of Hazael, and it will devour the fortresses of Ben Hadad.
5 Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
I will break the gate bars of Damascus and cut off the man who rules over the Valley of Aven, and also the man who holds the scepter in Beth Eden. The people of Aram will go in captivity to Kir,” says Yahweh.
6 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
This is what Yahweh says: “For three sins of Gaza, even for four, I will not turn away punishment, because they carried away captive a whole people, to hand them over to Edom.
7 Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
I will send fire on the walls of Gaza, and it will devour her fortresses.
8 Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
I will cut off the man who lives in Ashdod and the man who holds the scepter from Ashkelon. I will turn my hand against Ekron, and the rest of the Philistines will perish,” says the Lord Yahweh.
9 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
This is what Yahweh says: “For three sins of Tyre, even for four, I will not turn away punishment, because they had delivered up a whole people to Edom, and they broke their covenant of brotherhood.
10 zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
I will send fire on the walls of Tyre, and it will devour her fortresses.”
11 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
This is what Yahweh says, “For three sins of Edom, even for four, I will not turn away punishment, because he pursued his brother with the sword and cast off all pity. His anger raged continually, and his wrath lasted forever.
12 Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
I will send fire on Teman, and it will devour the palaces of Bozrah.”
13 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
This is what Yahweh says, “For three sins of the people of Ammon, even for four, I will not turn away punishment, because they ripped open the pregnant women of Gilead, that they may enlarge their borders.
14 Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
I will light a fire in the walls of Rabbah, and it will devour the palaces, with a shout in the day of battle, with a tempest in the day of the whirlwind.
15 Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.
Their king will go into captivity, he and his officials together,” says Yahweh.