< Amos 1 >
1 Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
The words of Amos, who was among the herdmen of Tekoa, which he saw concerning Israel in the days of Uzziah king of Judah, and in the days of Jeroboam the son of Joash, king of Israel, two years before the earthquake.
2 Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
And he said, Jehovah roareth from Zion, and uttereth his voice from Jerusalem; and the pastures of the shepherds mourn, and the top of Carmel withereth.
3 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
Thus saith Jehovah: For three transgressions of Damascus, and for four, I will not revoke [my sentence], because they have threshed Gilead with threshing instruments of iron.
4 zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
And I will send a fire into the house of Hazael, and it shall devour the palaces of Ben-Hadad.
5 Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
And I will break the bar of Damascus, and cut off the inhabitant from the valley of Aven, and him that holdeth the sceptre from Beth-Eden; and the people of Syria shall go into captivity unto Kir, saith Jehovah.
6 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
Thus saith Jehovah: For three transgressions of Gazah, and for four, I will not revoke its sentence; because they carried away captive the whole captivity, to deliver [them] up to Edom.
7 Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
And I will send a fire on the wall of Gazah, and it shall devour the palaces thereof.
8 Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And I will cut off the inhabitant from Ashdod, and him that holdeth the sceptre from Ashkelon, and I will turn my hand against Ekron; and the remnant of the Philistines shall perish, saith the Lord Jehovah.
9 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
Thus saith Jehovah: For three transgressions of Tyre, and for four, I will not revoke its sentence; because they delivered up the whole captivity to Edom, and remembered not the brotherly covenant.
10 zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
And I will send a fire on the wall of Tyre, and it shall devour the palaces thereof.
11 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
Thus saith Jehovah: For three transgressions of Edom, and for four, I will not revoke its sentence; because he pursued his brother with the sword, and cast off all pity; and his anger did tear continually, and he kept his wrath for ever.
12 Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
And I will send a fire upon Teman, and it shall devour the palaces of Bozrah.
13 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
Thus saith Jehovah: For three transgressions of the children of Ammon, and for four, I will not revoke its sentence; because they ripped up the women with child of Gilead, that they might enlarge their border.
14 Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
And I will kindle a fire in the wall of Rabbah, and it shall devour the palaces thereof, with shouting in the day of battle, with a tempest in the day of the whirlwind.
15 Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.
And their king shall go into captivity, he and his princes together, saith Jehovah.