< Amos 1 >
1 Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
De Ord, som Amos, der var iblandt Hyrderne fra Thekoa, saa over Israel i Judas Konge Ussias's Dage og i Israels Konge Jeroboams, Joas's Søns, Dag, to Aar før Jordskælvet.
2 Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
Han sagde da: Herren skal brøle fra Zion og lade sin Røst lyde fra Jerusalem; og Hyrdernes Græsgange skulle sørge og Karmels Top blive tør.
3 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
Saa siger Herren: For tre Overtrædelser af Damaskus og for fire jeg tager det ikke tilbage — fordi de have tærsket Gilead med Jerntærskevogne,
4 zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
derfor vil jeg sende en Ild i Hasaels Hus, og den skal fortære Benhadads Paladser.
5 Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
Og jeg vil sønderbryde Portstængerne for Damaskus og udrydde Indbyggerne fra Avens Dal og den, som fører Spiret, fra Beth-Eden; og Syriens Folk skal bortføres til Kir, siger Herren.
6 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
Saa siger Herren: For tre Overtrædelser af Gaza og for fire — jeg tager det ikke tilbage fordi de have bortført de fangne alle til Hobe, for at overgive dem til Edom,
7 Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
derfor vil jeg sende en Ild paa Gazas Mur, og den skal fortære dens Paladser.
8 Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Og jeg vil udrydde Indbyggerne fra Asdod og den, som fører Spiret, fra Askalon; og jeg vil vende min Haand imod Ekron, og de overblevne af Filisterne skulle omkomme, siger den Herre, Herre.
9 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
Saa siger Herren: For tre Overtrædelser af Tyrus og for fire — jeg tager det ikke tilbage — fordi de overgave de bortførte alle til Hobe til Edom, og de kom ikke Broderpagten i Hu,
10 zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
derfor vil jeg sende en Ild paa Tyrus's Mur, og den skal fortære dens Paladser.
11 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
Saa siger Herren: For tre Overtrædelser af Edom og for fire — leg tager det ikke tilbage — fordi nan forfulgte sin Broder med Sværdet og kvalte sin Barmhjertighed, Saa at hans Vrede altid sønderrev, og han har bevaret sin Harme evindelig,
12 Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
derfor vil jeg sende en Ild i Theman, og den skal fortære Bozras Paladser.
13 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
Saa siger Herren: For tre Overtrædelser af Ammons Børn og for fire — jeg tager det ikke tilbage — fordi de sønderrev e de frugtsommelige i Gilead for at udvide deres Landemærke,
14 Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
derfor vil jeg antænde en Ild paa Rabbas Mur, og den skal fortære dens Paladser under Stormraab paa Krigens Dag, under Storm paa Hvirvelvindens Dag.
15 Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.
Og deres Konge skal vandre i Landflygtighed, han og hans Fyrster til Hobe, siger Herren.