< Amos 9 >

1 Na ga Ubangiji yana tsaye a gaban bagade, ya kuma ce, “Bugi kan ginshiƙan don madogaran ƙofa su girgiza. Saukar da su a kan dukan mutane; waɗanda ba su mutu ba zan kashe su da takobi. Ba mutum guda da zai tsere, babu wani da zai tsira.
Eu vi o Senhor de pé ao lado do altar, e ele disse: “Bata no topo dos pilares, para que as soleiras se abanem”. Quebrá-los em pedaços na cabeça de todos eles”. Matarei o último deles com a espada”. Nem um deles fugirá. Nem um deles escapará.
2 Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari, daga can hannuna zai fitar da su. Ko da sun hau can sama daga can zan sauko da su. (Sheol h7585)
Embora eles cavem no Sheol, lá minha mão os levará; e embora eles subam ao céu, lá os derrubarei. (Sheol h7585)
3 Ko da sun ɓuya a bisa Karmel, a can zan farauce su in cafko. Ko da sun ɓuya can ƙarƙashin teku, a can zan umarci maciji yă sare su.
Embora se escondam no topo do Carmelo, eu os procurarei e os tirarei dali; e embora estejam escondidos de minha vista no fundo do mar, ali eu comandarei a serpente, e ela os morderá.
4 Ko da abokan gābansu sun kore su zuwa zaman bauta, a can zan umarci takobi yă kashe su. “Zan sa musu ido don mugunta ba don alheri ba.”
Embora eles vão para o cativeiro diante de seus inimigos, lá eu comandarei a espada, e ela os matará. Colocarei meus olhos sobre eles para o mal, e não para o bem.
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, shi da yakan taɓa ƙasa sai ta narke, kuma dukan mazauna cikinta suna makoki, ƙasar gaba ɗaya takan hau ta kuma sauka kamar Nilu, sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar,
Pois o Senhor, Javé dos Exércitos, é aquele que toca a terra e ela derrete, e todos os que nela habitam lamentarão; e ela se levantará totalmente como o rio, e afundará novamente, como o rio do Egito.
6 shi da ya gina kyakkyawar fadarsa a cikin sammai ya kuma kafa harsashenta a duniya, shi da yakan kira ruwan teku yă kuma kwarara su a bisa duniya, Ubangiji ne sunansa.
É aquele que constrói seus quartos nos céus, e fundou sua abóbada na terra; é aquele que clama pelas águas do mar, e as derrama sobre a superfície da terra - Yahweh é seu nome.
7 “Ku ba Isra’ilawa ba ne, daidai gare ni kamar yadda Kushawa suke?” In ji Ubangiji. “Ban fito da Isra’ila daga Masar ba, Filistiyawa kuma daga Kaftor Arameyawa kuma daga Kir ba?
Não são vocês como os filhos dos etíopes para mim, filhos de Israel?” diz Yahweh. “Eu não trouxe Israel da terra do Egito, e os filisteus de Caphtor, e os sírios de Kir?
8 “Tabbatacce idanun Ubangiji Mai Iko Duka suna a kan mulkin nan mai zunubi. Zan hallaka shi daga fuskar duniya, duk da haka ba zan hallaka gidan Yaƙub ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji.
Eis que os olhos do Senhor Javé estão sobre o reino pecaminoso, e eu o destruirei da superfície da terra, exceto que não destruirei totalmente a casa de Jacó”, diz Javé.
9 “Gama zan ba da umarni, zan kuma tankaɗe gidan Isra’ila a cikin dukan ƙasashe kamar yadda ake tankaɗe hatsi a cikin matankaɗi kuma ko ƙwaya ɗaya ba za tă fāɗi a ƙasa ba.
“Pois eis que eu mandarei, e peneirarei a casa de Israel entre todas as nações como se peneiram grãos em uma peneira, mas não cairá o menor grão sobre a terra”.
10 Dukan masu zunubi a cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, wato, su masu cewa, ‘Masifa ba za tă fāɗo ko ta same mu ba.’
Todos os pecadores de meu povo morrerão pela espada, que dizem: 'O mal não nos alcançará nem nos encontrará'.
11 “A wannan rana zan maido da tentin Dawuda da ya fāɗi. Zan gyaggyara wuraren da suka yayyage, in kuma maido da kufansa in gina shi kamar yadda yake a dā,
Nesse dia levantarei a tenda de David que caiu e fecharei suas brechas, e levantarei suas ruínas, e a construirei como nos velhos tempos,
12 domin su mallaki raguwar Edom da duk al’ummai da suke amsa sunana,” in ji Ubangiji shi wanda zai yi waɗannan abubuwa.
para que eles possam possuir o remanescente de Edom e todas as nações que são chamadas pelo meu nome”, diz Yahweh que faz isso.
13 “Ranaku suna zuwa, in ji Ubangiji, “sa’ad da mai huɗa zai sha gaban mai girbi mai shuki kuma yă bi bayan mai matsin inabi. Sabon ruwan inabi zai ɗiga daga duwatsu yă kuma kwararo daga tuddai.
“Eis que os dias vêm”, diz Yahweh, “que o lavrador deve ultrapassar o ceifeiro”, e o que pisa uvas aquele que semeia sementes; e o vinho doce vai pingar das montanhas, e fluem das colinas.
14 Zan dawo da waɗanda aka kai zaman bauta mutanena Isra’ila. “Za su sāke gina biranen da suke kango su kuma zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi su kuma sha ruwan inabinsu; za su yi lambuna su kuma ci amfaninsu.
Vou trazer meu povo Israel de volta do cativeiro, e eles reconstruirão as cidades arruinadas, e as habitarão; e eles plantarão vinhedos e beberão vinho deles. Eles também devem fazer jardins, e comer suas frutas.
15 Zan dasa Isra’ila a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumɓuke su daga ƙasar da na ba su ba,” in ji Ubangiji Allahnku.
Eu os plantarei em suas terras, e eles não serão mais arrancados de suas terras que eu lhes dei”. diz Yahweh seu Deus.

< Amos 9 >