< Amos 9 >

1 Na ga Ubangiji yana tsaye a gaban bagade, ya kuma ce, “Bugi kan ginshiƙan don madogaran ƙofa su girgiza. Saukar da su a kan dukan mutane; waɗanda ba su mutu ba zan kashe su da takobi. Ba mutum guda da zai tsere, babu wani da zai tsira.
Ngabona iNkosi imi phezu kwelathi, yathi: Tshaya isihloko ukuze imibundu inyikinyeke, ubaqume ekhanda, bonke babo; labokucina babo ngibabulale ngenkemba; kakuyikubaleka obalekayo wabo, kakuyikuphunyuka ophunyukayo wabo.
2 Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari, daga can hannuna zai fitar da su. Ko da sun hau can sama daga can zan sauko da su. (Sheol h7585)
Loba begebha besiya esihogweni, isandla sami sizabathatha khona; loba bekhwela-ke besiya emazulwini, ngizabehlisa khona; (Sheol h7585)
3 Ko da sun ɓuya a bisa Karmel, a can zan farauce su in cafko. Ko da sun ɓuya can ƙarƙashin teku, a can zan umarci maciji yă sare su.
loba becatsha-ke engqongeni yeKharmeli, ngizabadinga ngibathathe khona; loba becatsha-ke basuke phambi kwamehlo ami kuphansi yolwandle, ngizalaya inyoka ivela lapho ezabaluma;
4 Ko da abokan gābansu sun kore su zuwa zaman bauta, a can zan umarci takobi yă kashe su. “Zan sa musu ido don mugunta ba don alheri ba.”
loba besiya-ke ekuthunjweni phambi kwezitha zabo, ngizalaya inkemba ivela lapho ukuze izebabulala; ngimise ilihlo lami phezu kwabo ngokubi, hatshi-ke ngokuhle.
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, shi da yakan taɓa ƙasa sai ta narke, kuma dukan mazauna cikinta suna makoki, ƙasar gaba ɗaya takan hau ta kuma sauka kamar Nilu, sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar,
Njalo kuyiNkosi uJehova wamabandla ethinta umhlaba, ukuze uncibilike, balile bonke abahlala kuwo, ukhukhumale wonke njengomfula, utshone njengomfula weGibhithe.
6 shi da ya gina kyakkyawar fadarsa a cikin sammai ya kuma kafa harsashenta a duniya, shi da yakan kira ruwan teku yă kuma kwarara su a bisa duniya, Ubangiji ne sunansa.
Eyakha amakamelo ayo aphezulu emazulwini, yamisa amaviyo ayo emhlabeni, ebiza amanzi olwandle, iwathululele ebusweni bomhlaba; iNkosi libizo layo.
7 “Ku ba Isra’ilawa ba ne, daidai gare ni kamar yadda Kushawa suke?” In ji Ubangiji. “Ban fito da Isra’ila daga Masar ba, Filistiyawa kuma daga Kaftor Arameyawa kuma daga Kir ba?
Kimi kalinjengabantwana bamaEthiyopiya yini, lina bantwana bakoIsrayeli? itsho iNkosi. Kangikhuphulanga yini uIsrayeli elizweni leGibhithe, lamaFilisti eKafitori, lamaSiriya eKiri?
8 “Tabbatacce idanun Ubangiji Mai Iko Duka suna a kan mulkin nan mai zunubi. Zan hallaka shi daga fuskar duniya, duk da haka ba zan hallaka gidan Yaƙub ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji.
Khangela, amehlo eNkosi uJehova aphezu kombuso owonayo; njalo ngizawuchitha usuke ebusweni bomhlaba, kube kanti kangiyikuyichitha ngokupheleleyo indlu kaJakobe, itsho iNkosi.
9 “Gama zan ba da umarni, zan kuma tankaɗe gidan Isra’ila a cikin dukan ƙasashe kamar yadda ake tankaɗe hatsi a cikin matankaɗi kuma ko ƙwaya ɗaya ba za tă fāɗi a ƙasa ba.
Ngoba khangela, ngizalaya ngihlungule indlu kaIsrayeli phakathi kwazo zonke izizwe njengamabele ehlungulwa ngokhomane, kodwa kakuyikuwela emhlabathini ilitshe elincinyane.
10 Dukan masu zunubi a cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, wato, su masu cewa, ‘Masifa ba za tă fāɗo ko ta same mu ba.’
Zonke izoni zabantu bami zizakufa ngenkemba, ezithi: Okubi kakuyikufinyelela kithi kumbe kusihlangabeze.
11 “A wannan rana zan maido da tentin Dawuda da ya fāɗi. Zan gyaggyara wuraren da suka yayyage, in kuma maido da kufansa in gina shi kamar yadda yake a dā,
Ngalolosuku ngizavusa idumba likaDavida eliwileyo, ngivale izikhala zalo, ngivuse amanxiwa alo, ngilakhe njengensukwini zendulo;
12 domin su mallaki raguwar Edom da duk al’ummai da suke amsa sunana,” in ji Ubangiji shi wanda zai yi waɗannan abubuwa.
ukuze badle ilifa lensali yeEdoma, lezizwe zonke ezibizwa ngebizo lami, itsho iNkosi eyenza lokhu.
13 “Ranaku suna zuwa, in ji Ubangiji, “sa’ad da mai huɗa zai sha gaban mai girbi mai shuki kuma yă bi bayan mai matsin inabi. Sabon ruwan inabi zai ɗiga daga duwatsu yă kuma kwararo daga tuddai.
Khangela, insuku ziyeza, itsho iNkosi, lapho olimayo ezasondela kovunayo, lonyathela izithelo zevini kohlanyela inhlanyelo; lentaba zizathonta iwayini elimnandi, lamaqaqa wonke ancibilike.
14 Zan dawo da waɗanda aka kai zaman bauta mutanena Isra’ila. “Za su sāke gina biranen da suke kango su kuma zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi su kuma sha ruwan inabinsu; za su yi lambuna su kuma ci amfaninsu.
Njalo ngizaphendula ukuthunjwa kwabantu bami uIsrayeli, bayakhe imizi echithekileyo, bahlale kiyo; bahlanyele izivini, banathe iwayini lazo, benze izivande, badle izithelo zazo.
15 Zan dasa Isra’ila a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumɓuke su daga ƙasar da na ba su ba,” in ji Ubangiji Allahnku.
Ngibahlanyele elizweni labo, bangabe besasitshulwa elizweni engibanike lona, itsho iNkosi uNkulunkulu wakho.

< Amos 9 >