< Amos 9 >
1 Na ga Ubangiji yana tsaye a gaban bagade, ya kuma ce, “Bugi kan ginshiƙan don madogaran ƙofa su girgiza. Saukar da su a kan dukan mutane; waɗanda ba su mutu ba zan kashe su da takobi. Ba mutum guda da zai tsere, babu wani da zai tsira.
Ngabona uThixo emi phansi kwe-alithari, wasesithi: “Tshaya izihloko zensika ukuze imibundu inyikinyeke. Ziwisele phansi phezu kwamakhanda abantu bonke; labo abazasala ngizababulala ngenkemba. Kakho lamunye ozaphunyuka, kakho ozabaleka.
2 Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari, daga can hannuna zai fitar da su. Ko da sun hau can sama daga can zan sauko da su. (Sheol )
Loba besimba baze bafike ekudepheni kwengcwaba, isandla sami sizabathatha khonapho. Loba bekhwela baye phezulu emazulwini, bekhonapho ngizabehlisela phansi. (Sheol )
3 Ko da sun ɓuya a bisa Karmel, a can zan farauce su in cafko. Ko da sun ɓuya can ƙarƙashin teku, a can zan umarci maciji yă sare su.
Loba becatsha engqongweni yeKhameli, khonapho ngizabadinga ngibabambe. Loba bengicatshela enzikini yolwandle, khonapho ngizalaya inyoka ukuba ibalume.
4 Ko da abokan gābansu sun kore su zuwa zaman bauta, a can zan umarci takobi yă kashe su. “Zan sa musu ido don mugunta ba don alheri ba.”
Loba izitha zabo zingabasa ekuthunjweni, khonale ngizalaya inkemba ukuba ibabulale. Ngizagxilisa amehlo ami kubo ngenxa yobubi hatshi ngobuhle.”
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, shi da yakan taɓa ƙasa sai ta narke, kuma dukan mazauna cikinta suna makoki, ƙasar gaba ɗaya takan hau ta kuma sauka kamar Nilu, sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar,
INkosi, uThixo uSomandla, yena othinta umhlaba uncibilike, kuthi bonke abahlezi kuwo bakhale, ilizwe lonke liyaphakama njengoNayili liphinde litshone phansi njengomfula waseGibhithe,
6 shi da ya gina kyakkyawar fadarsa a cikin sammai ya kuma kafa harsashenta a duniya, shi da yakan kira ruwan teku yă kuma kwarara su a bisa duniya, Ubangiji ne sunansa.
yena owakha indlu yakhe yobukhosi ephakemeyo emazulwini njalo ubeka isisekelo sakhe phezu komhlaba, ebiza amanzi olwandle awathele phezu kobuso bomhlaba, uThixo yilo ibizo lakhe.
7 “Ku ba Isra’ilawa ba ne, daidai gare ni kamar yadda Kushawa suke?” In ji Ubangiji. “Ban fito da Isra’ila daga Masar ba, Filistiyawa kuma daga Kaftor Arameyawa kuma daga Kir ba?
“Lina ma-Israyeli, kimi kalinjengamaKhushi na?” kutsho uThixo. “U-Israyeli kangimkhuphanga eGibhithe, lamaFilistiya eKhafithori, kanye lama-Aramu eKhiri na?
8 “Tabbatacce idanun Ubangiji Mai Iko Duka suna a kan mulkin nan mai zunubi. Zan hallaka shi daga fuskar duniya, duk da haka ba zan hallaka gidan Yaƙub ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji.
Impela amehlo kaThixo Wobukhosi aphezu kombuso olesono. Ngizawukhucula ebusweni bomhlaba ikanti indlu kaJakhobe angiyikuyichitha ngokupheleleyo,” kutsho uThixo.
9 “Gama zan ba da umarni, zan kuma tankaɗe gidan Isra’ila a cikin dukan ƙasashe kamar yadda ake tankaɗe hatsi a cikin matankaɗi kuma ko ƙwaya ɗaya ba za tă fāɗi a ƙasa ba.
“Ngoba ngizakupha umlayo, njalo ngizahlungula indlu ka-Israyeli phakathi kwezizwe zonke njengokuhlungulwa kwamabele ekhomaneni njalo akukho hlamvu oluzawela phansi.
10 Dukan masu zunubi a cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, wato, su masu cewa, ‘Masifa ba za tă fāɗo ko ta same mu ba.’
Izoni zonke phakathi kwabantu bami zizakufa ngenkemba, bonke labo abathi, ‘Umonakalo kawuyikusifica loba usihlangabeze.’”
11 “A wannan rana zan maido da tentin Dawuda da ya fāɗi. Zan gyaggyara wuraren da suka yayyage, in kuma maido da kufansa in gina shi kamar yadda yake a dā,
“Ngalolosuku ngizavusa ithente likaDavida elawayo. Ngizavala izikhala zalo, ngivuselele okwadilikayo kwalo, ngilakhe njengelaliyikho khona,
12 domin su mallaki raguwar Edom da duk al’ummai da suke amsa sunana,” in ji Ubangiji shi wanda zai yi waɗannan abubuwa.
ukuze bathathe insalela ye-Edomi kanye lezizwe zonke ezizabizwa ngebizo lami,” kutsho uThixo, ozazenza lezizinto.
13 “Ranaku suna zuwa, in ji Ubangiji, “sa’ad da mai huɗa zai sha gaban mai girbi mai shuki kuma yă bi bayan mai matsin inabi. Sabon ruwan inabi zai ɗiga daga duwatsu yă kuma kwararo daga tuddai.
UThixo uthi, “Zinsuku ziyeza, lapho ovunayo ezaficwa ngolimayo, lohlanyelayo aficwe ngokhama amavini. Iwayini elitsha lizagobhoza ezintabeni, njalo ligeleze emaqaqeni wonke.
14 Zan dawo da waɗanda aka kai zaman bauta mutanena Isra’ila. “Za su sāke gina biranen da suke kango su kuma zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi su kuma sha ruwan inabinsu; za su yi lambuna su kuma ci amfaninsu.
Ngizababuyisela abantu bami bako-Israyeli abathunjwayo. Bazawakha kutsha amadolobho adilikayo bahlale kuwo. Bazahlanyela izivini banathe iwayini lazo; bazakwenza izivande badle izithelo zazo.
15 Zan dasa Isra’ila a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumɓuke su daga ƙasar da na ba su ba,” in ji Ubangiji Allahnku.
Ngizagxumeka u-Israyeli elizweni lakhe angaphindi asitshunwe futhi elizweni engimnike lona,” kutsho uThixo uNkulunkulu wenu.