< Amos 9 >
1 Na ga Ubangiji yana tsaye a gaban bagade, ya kuma ce, “Bugi kan ginshiƙan don madogaran ƙofa su girgiza. Saukar da su a kan dukan mutane; waɗanda ba su mutu ba zan kashe su da takobi. Ba mutum guda da zai tsere, babu wani da zai tsira.
I siy the Lord stondynge on the auter, and he seide, Smyte thou the herre, and the ouer threshfoldis be mouyd togidere; for aueryce is in the heed of alle, and Y schal sle bi swerd the laste of hem; ther schal no fliyt be to hem, and he that schal fle of hem, schal not be sauyd.
2 Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari, daga can hannuna zai fitar da su. Ko da sun hau can sama daga can zan sauko da su. (Sheol )
If thei schulen go doun til to helle, fro thennus myn hond schal lede out hem; and if thei schulen `stie til in to heuene, fro thennus Y schal drawe hem doun. (Sheol )
3 Ko da sun ɓuya a bisa Karmel, a can zan farauce su in cafko. Ko da sun ɓuya can ƙarƙashin teku, a can zan umarci maciji yă sare su.
And if thei schulen be hid in the cop of Carmele, fro thennus Y sekynge schal do awei hem; and if thei schulen hide hem silf fro myn iyen in the depnesse of the see, there Y shal comaunde to a serpente, and it schal bite hem.
4 Ko da abokan gābansu sun kore su zuwa zaman bauta, a can zan umarci takobi yă kashe su. “Zan sa musu ido don mugunta ba don alheri ba.”
And if thei schulen go awei in to caitifte bifore her enemyes, there Y schal comaunde to swerd, and it schal sle hem. And Y schal putte myn iyen on hem in to yuel, and not in to good.
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, shi da yakan taɓa ƙasa sai ta narke, kuma dukan mazauna cikinta suna makoki, ƙasar gaba ɗaya takan hau ta kuma sauka kamar Nilu, sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar,
And the Lord God of oostis schal do these thingis, that touchith erthe, and it schal faile, and alle men dwellynge ther ynne schulen mourene; and it schal stie vp as ech stronde, and it schal flete awei as flood of Egipt.
6 shi da ya gina kyakkyawar fadarsa a cikin sammai ya kuma kafa harsashenta a duniya, shi da yakan kira ruwan teku yă kuma kwarara su a bisa duniya, Ubangiji ne sunansa.
He that bildith his stiyng vp in heuene, schal do these thingis, and foundide his birthun on erthe; which clepith watris of the see, and heldith out hem on the face of erthe; the Lord is name of hym.
7 “Ku ba Isra’ilawa ba ne, daidai gare ni kamar yadda Kushawa suke?” In ji Ubangiji. “Ban fito da Isra’ila daga Masar ba, Filistiyawa kuma daga Kaftor Arameyawa kuma daga Kir ba?
Whether not as sones of Ethiopiens ye ben to me, the sones of Israel? seith the Lord God. Whether Y made not Israel for to stie vp fro the lond of Egipt, and Palestines fro Capodosie, and Siriens fro Cirenen?
8 “Tabbatacce idanun Ubangiji Mai Iko Duka suna a kan mulkin nan mai zunubi. Zan hallaka shi daga fuskar duniya, duk da haka ba zan hallaka gidan Yaƙub ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji.
Lo! the iyen of the Lord God ben on the rewme synnynge, and Y schal al to-breke it fro the face of erthe; netheles Y al to-brekynge schal not al to-breke the hous of Jacob, seith the Lord.
9 “Gama zan ba da umarni, zan kuma tankaɗe gidan Isra’ila a cikin dukan ƙasashe kamar yadda ake tankaɗe hatsi a cikin matankaɗi kuma ko ƙwaya ɗaya ba za tă fāɗi a ƙasa ba.
For lo! Y schal comaunde, and schal schake the hous of Israel in alle folkis, as wheete is in a riddil, and a litil stoon schal not falle on erthe.
10 Dukan masu zunubi a cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, wato, su masu cewa, ‘Masifa ba za tă fāɗo ko ta same mu ba.’
Alle synneris of my puple schulen die bi swerd, whiche seien, Yuel schal not neiy, and schal not come on vs.
11 “A wannan rana zan maido da tentin Dawuda da ya fāɗi. Zan gyaggyara wuraren da suka yayyage, in kuma maido da kufansa in gina shi kamar yadda yake a dā,
In that dai Y schal reise the tabernacle of Dauith, that felle doun, and Y schal ayen bilde openyngis of wallis therof, and Y schal restore the thingis that fellen doun; and Y schal ayen bilde it,
12 domin su mallaki raguwar Edom da duk al’ummai da suke amsa sunana,” in ji Ubangiji shi wanda zai yi waɗannan abubuwa.
as in olde daies, that thei welde the remenauntis of Idume, and alle naciouns; for that my name is clepun to help on hem, seith the Lord doynge these thingis.
13 “Ranaku suna zuwa, in ji Ubangiji, “sa’ad da mai huɗa zai sha gaban mai girbi mai shuki kuma yă bi bayan mai matsin inabi. Sabon ruwan inabi zai ɗiga daga duwatsu yă kuma kwararo daga tuddai.
Lo! daies comen, seith the Lord, and the erere schal take the repere, and `the stampere of grape schal take the man sowynge seed; and mounteyns schulen droppe swetnesse, and alle smale hillis schulen be tilid.
14 Zan dawo da waɗanda aka kai zaman bauta mutanena Isra’ila. “Za su sāke gina biranen da suke kango su kuma zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi su kuma sha ruwan inabinsu; za su yi lambuna su kuma ci amfaninsu.
And Y schal conuerte the caitifte of my puple Israel, and thei schulen bilde forsakun citees, and schulen dwelle; and schulen plaunte vyneyerdis, and thei schulen drynke wyn of hem; and schulen make gardyns, and schulen ete fruitis of hem.
15 Zan dasa Isra’ila a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumɓuke su daga ƙasar da na ba su ba,” in ji Ubangiji Allahnku.
And Y schal plaunte hem on her lond, and Y schal no more drawe out hem of her lond, which Y yaf to hem, seith the Lord thi God.