< Amos 9 >

1 Na ga Ubangiji yana tsaye a gaban bagade, ya kuma ce, “Bugi kan ginshiƙan don madogaran ƙofa su girgiza. Saukar da su a kan dukan mutane; waɗanda ba su mutu ba zan kashe su da takobi. Ba mutum guda da zai tsere, babu wani da zai tsira.
Yahweh [showed me another vision. In the vision, ] I saw him standing next to the altar. He said, “Shake the tops of the pillars [of the temple], until they become loose and fall down, so that even the foundation will shake. Then cause the [pieces of the temple] to fall down on the people [who are inside]. I will kill with a sword anyone who [tries to] flee; no one will escape.
2 Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari, daga can hannuna zai fitar da su. Ko da sun hau can sama daga can zan sauko da su. (Sheol h7585)
If they dig deep pits in the ground, or if they try to climb up to the sky [in order to escape], I will reach out and grab them. (Sheol h7585)
3 Ko da sun ɓuya a bisa Karmel, a can zan farauce su in cafko. Ko da sun ɓuya can ƙarƙashin teku, a can zan umarci maciji yă sare su.
If they go to the top of Carmel [Mountain] to escape, I will search for them and seize them. If they [try to] hide from me at the bottom of the sea, I will command the [huge] sea monster to bite them.
4 Ko da abokan gābansu sun kore su zuwa zaman bauta, a can zan umarci takobi yă kashe su. “Zan sa musu ido don mugunta ba don alheri ba.”
If their enemies [capture them and] force them to go to other countries, I will command that they be killed there with swords. I am determined [IDM] to get rid of them, not to help them.”
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, shi da yakan taɓa ƙasa sai ta narke, kuma dukan mazauna cikinta suna makoki, ƙasar gaba ɗaya takan hau ta kuma sauka kamar Nilu, sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar,
When the Commander of the armies of angels touches the earth, it melts, and all over the earth [many people die, and the others] mourn for them. [It is as though] Yahweh causes the earth repeatedly to rise and fall like [SIM] the Nile [River] rises and falls.
6 shi da ya gina kyakkyawar fadarsa a cikin sammai ya kuma kafa harsashenta a duniya, shi da yakan kira ruwan teku yă kuma kwarara su a bisa duniya, Ubangiji ne sunansa.
He builds his [beautiful] palace in heaven, and sets/causes the sky to be like a dome over the earth. He scoops up the water from the ocean and [puts it into clouds], and then empties [the clouds] onto the earth. His name is Yahweh.
7 “Ku ba Isra’ilawa ba ne, daidai gare ni kamar yadda Kushawa suke?” In ji Ubangiji. “Ban fito da Isra’ila daga Masar ba, Filistiyawa kuma daga Kaftor Arameyawa kuma daga Kir ba?
And Yahweh says, “You people of Israel, you are certainly [RHQ] [now no more important to me] than the people of Ethiopia. I brought your [ancestors] here from Egypt, but I also brought the people of Philistia from Crete [Island], and I brought the people of Syria from the Kir [region].
8 “Tabbatacce idanun Ubangiji Mai Iko Duka suna a kan mulkin nan mai zunubi. Zan hallaka shi daga fuskar duniya, duk da haka ba zan hallaka gidan Yaƙub ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji.
I [SYN], Yahweh the Lord, have seen that you people in the kingdom [of Israel] are very sinful, so I will (destroy you/wipe you off the earth). But I will not get rid of all you descendants [MTY] of Jacob. [That is what will surely happen because] I, Yahweh, have said it.
9 “Gama zan ba da umarni, zan kuma tankaɗe gidan Isra’ila a cikin dukan ƙasashe kamar yadda ake tankaɗe hatsi a cikin matankaɗi kuma ko ƙwaya ɗaya ba za tă fāɗi a ƙasa ba.
When I command it, [it will be as though] I will shake you Israeli people [who are living] in various nations, like [MET] [a farmer] shakes a sieve [to separate] the stone pebbles [from the grain], in order that they do not fall on the ground [with the grain].
10 Dukan masu zunubi a cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, wato, su masu cewa, ‘Masifa ba za tă fāɗo ko ta same mu ba.’
From among my people, all you sinful people who say, ‘We will not experience disasters; nothing evil will happen to us,’ will be killed by [your enemies’] swords.”
11 “A wannan rana zan maido da tentin Dawuda da ya fāɗi. Zan gyaggyara wuraren da suka yayyage, in kuma maido da kufansa in gina shi kamar yadda yake a dā,
“The kingdom [over which King] David [ruled has been destroyed, like] [MET] a house that collapsed and then became ruins. But some day I will cause it to be a kingdom again. I will cause it to prosper again just like it did previously.
12 domin su mallaki raguwar Edom da duk al’ummai da suke amsa sunana,” in ji Ubangiji shi wanda zai yi waɗannan abubuwa.
When that happens, your [armies] will seize/capture the remaining part of Edom [region] again, and they will also seize the land in other nations that previously belonged to me [MTY]. I, Yahweh, have said [that I will do these things], and I will certainly cause them to happen.
13 “Ranaku suna zuwa, in ji Ubangiji, “sa’ad da mai huɗa zai sha gaban mai girbi mai shuki kuma yă bi bayan mai matsin inabi. Sabon ruwan inabi zai ɗiga daga duwatsu yă kuma kwararo daga tuddai.
There will be a time [when your crops will grow very well]. Very soon after the crops are harvested, farmers will plow the ground [to plant more crops in it again], and soon after the vineyards are planted, [farmers will harvest] grapes and tread on them [to make wine]. [And because there will be a lot of] wine, [it will seem as though] wine is flowing down from the hills [DOU].
14 Zan dawo da waɗanda aka kai zaman bauta mutanena Isra’ila. “Za su sāke gina biranen da suke kango su kuma zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi su kuma sha ruwan inabinsu; za su yi lambuna su kuma ci amfaninsu.
I will cause you, my Israeli people, to prosper again. You will rebuild your towns and live in them. You will plant vineyards and then drink the wine [made from the grapes that grows in them].
15 Zan dasa Isra’ila a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumɓuke su daga ƙasar da na ba su ba,” in ji Ubangiji Allahnku.
I will enable you to live [MET] in your land again, the land that I gave to [your ancestors], and never again will you be forced to leave it. [That is what will surely happen because] I, Yahweh, have said it.”

< Amos 9 >