< Amos 9 >

1 Na ga Ubangiji yana tsaye a gaban bagade, ya kuma ce, “Bugi kan ginshiƙan don madogaran ƙofa su girgiza. Saukar da su a kan dukan mutane; waɗanda ba su mutu ba zan kashe su da takobi. Ba mutum guda da zai tsere, babu wani da zai tsira.
I saw the Lord standing upon the altar; and he said, Smite the capital, that the sills may quake; and break them in pieces over the head of all of them; and their posterity will I slay with the sword: there shall not flee away from them one that fleeth, and there shall not escape from them one that is saved.
2 Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari, daga can hannuna zai fitar da su. Ko da sun hau can sama daga can zan sauko da su. (Sheol h7585)
Though they were to creep down into the nether world, thence would my hand fetch them; and though they were to climb up to the heavens, thence would I bring them down; (Sheol h7585)
3 Ko da sun ɓuya a bisa Karmel, a can zan farauce su in cafko. Ko da sun ɓuya can ƙarƙashin teku, a can zan umarci maciji yă sare su.
And though they were to hide themselves on the top of Carmel, thence would I search and take them out; and though they were to conceal themselves from before my eyes in the bottom of the sea, thence would I command the serpent, that he should bite them;
4 Ko da abokan gābansu sun kore su zuwa zaman bauta, a can zan umarci takobi yă kashe su. “Zan sa musu ido don mugunta ba don alheri ba.”
And though they were to go into captivity before their enemies, thence would I command the sword, that it should slay them: and I will set my eye upon them for evil, and not for good.
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, shi da yakan taɓa ƙasa sai ta narke, kuma dukan mazauna cikinta suna makoki, ƙasar gaba ɗaya takan hau ta kuma sauka kamar Nilu, sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar,
And the Lord Eternal of hosts it is that toucheth the earth, and she melteth away, and all that dwell thereon shall mourn; and she riseth up like a stream wholly; and she sinketh like the stream of Egypt;
6 shi da ya gina kyakkyawar fadarsa a cikin sammai ya kuma kafa harsashenta a duniya, shi da yakan kira ruwan teku yă kuma kwarara su a bisa duniya, Ubangiji ne sunansa.
That buildeth in the heavens his steps, and hath founded his vault over the earth; that calleth for the waters of the sea, and poureth them out over the face of the earth: The Lord is his name.
7 “Ku ba Isra’ilawa ba ne, daidai gare ni kamar yadda Kushawa suke?” In ji Ubangiji. “Ban fito da Isra’ila daga Masar ba, Filistiyawa kuma daga Kaftor Arameyawa kuma daga Kir ba?
Are ye not like the children of the Ethiopians unto me, O children of Israel? saith the Lord: have I not brought up Israel out of the land of Egypt? and the Philistines from Caphtor, and the Syrians from Kir?
8 “Tabbatacce idanun Ubangiji Mai Iko Duka suna a kan mulkin nan mai zunubi. Zan hallaka shi daga fuskar duniya, duk da haka ba zan hallaka gidan Yaƙub ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji.
Behold, the eyes of the Lord Eternal are upon the sinful kingdom, and I will destroy it from off the face of the earth; save only that I will not utterly destroy the house of Jacob, saith the Lord.
9 “Gama zan ba da umarni, zan kuma tankaɗe gidan Isra’ila a cikin dukan ƙasashe kamar yadda ake tankaɗe hatsi a cikin matankaɗi kuma ko ƙwaya ɗaya ba za tă fāɗi a ƙasa ba.
For, lo, I will give the command, and I will shake about among all the nations the house of Israel, as one shaketh things in a sieve, while not the least piece falleth down upon the earth.
10 Dukan masu zunubi a cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, wato, su masu cewa, ‘Masifa ba za tă fāɗo ko ta same mu ba.’
By the sword shall die all the sinners of my people, who say, The evil will not come near [us], nor hasten along for our sake.
11 “A wannan rana zan maido da tentin Dawuda da ya fāɗi. Zan gyaggyara wuraren da suka yayyage, in kuma maido da kufansa in gina shi kamar yadda yake a dā,
On that day will I raise up the tabernacle of David which is fallen; and I will close up its breaches; and its ruins will I raise up, and I will rebuild it as in days of old:
12 domin su mallaki raguwar Edom da duk al’ummai da suke amsa sunana,” in ji Ubangiji shi wanda zai yi waɗannan abubuwa.
In order that they may take possession of the remnant of Edom, and of all the nations, which are called by my name, saith the Lord that doth this.
13 “Ranaku suna zuwa, in ji Ubangiji, “sa’ad da mai huɗa zai sha gaban mai girbi mai shuki kuma yă bi bayan mai matsin inabi. Sabon ruwan inabi zai ɗiga daga duwatsu yă kuma kwararo daga tuddai.
Behold, days are coming, saith the Lord, when the ploughman shall come close up to the harvester, and the treader of the grapes to the one that scattereth the seed: and the mountains shall drop with sweet new wine, and all the hills shall melt away.
14 Zan dawo da waɗanda aka kai zaman bauta mutanena Isra’ila. “Za su sāke gina biranen da suke kango su kuma zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi su kuma sha ruwan inabinsu; za su yi lambuna su kuma ci amfaninsu.
And I will bring back the captivity of my people Israel, and they shall build the wasted cities, and dwell therein; and they shall plant vineyards, and drink their wine; and they shall lay out gardens, and eat their fruit.
15 Zan dasa Isra’ila a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumɓuke su daga ƙasar da na ba su ba,” in ji Ubangiji Allahnku.
And I will plant them upon their own soil, and they shall not be pulled up any more out of their land which I have given unto them, saith the Lord thy God.

< Amos 9 >