< Amos 9 >

1 Na ga Ubangiji yana tsaye a gaban bagade, ya kuma ce, “Bugi kan ginshiƙan don madogaran ƙofa su girgiza. Saukar da su a kan dukan mutane; waɗanda ba su mutu ba zan kashe su da takobi. Ba mutum guda da zai tsere, babu wani da zai tsira.
I saw the Lord standing over an altar, and he said: “Strike the hinges, and let the lintels be shaken. For there is avarice at the head of them all, and I will execute the very last of them with the sword. There will be no escape for them. They will flee, and he who flees from among them will not be saved.
2 Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari, daga can hannuna zai fitar da su. Ko da sun hau can sama daga can zan sauko da su. (Sheol h7585)
If they descend even to the underworld, from there my hand will draw them out; and if they ascend even to the sky, from there will I pull them down. (Sheol h7585)
3 Ko da sun ɓuya a bisa Karmel, a can zan farauce su in cafko. Ko da sun ɓuya can ƙarƙashin teku, a can zan umarci maciji yă sare su.
And if they were hiding at the top of Carmel, when searching there, I would steal them away, and if they conceal themselves from my eyes in the depths of the sea, I will command the serpent there and he will bite them.
4 Ko da abokan gābansu sun kore su zuwa zaman bauta, a can zan umarci takobi yă kashe su. “Zan sa musu ido don mugunta ba don alheri ba.”
And if they go into captivity in the sight of their enemies, there I will command the sword, and it will kill them. And I will set my eyes over them for harm and not for good.”
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, shi da yakan taɓa ƙasa sai ta narke, kuma dukan mazauna cikinta suna makoki, ƙasar gaba ɗaya takan hau ta kuma sauka kamar Nilu, sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar,
And the Lord God of hosts, he touches the earth and it will melt. And all who dwell in it will mourn. And everyone will rise up like a river, and will flow away like the river of Egypt.
6 shi da ya gina kyakkyawar fadarsa a cikin sammai ya kuma kafa harsashenta a duniya, shi da yakan kira ruwan teku yă kuma kwarara su a bisa duniya, Ubangiji ne sunansa.
He establishes his ascension into heaven, and he has founded his bundle on the earth. He calls the waters of the ocean, and pours them over the face of the earth. The Lord is his name.
7 “Ku ba Isra’ilawa ba ne, daidai gare ni kamar yadda Kushawa suke?” In ji Ubangiji. “Ban fito da Isra’ila daga Masar ba, Filistiyawa kuma daga Kaftor Arameyawa kuma daga Kir ba?
Sons of Israel, are you not like the sons of the Ethiopians to me, says the Lord? Did I not cause Israel to rise up out of the land of Egypt, and the Philistines out of Cappadocia, and the Syrians out of Cyrene?
8 “Tabbatacce idanun Ubangiji Mai Iko Duka suna a kan mulkin nan mai zunubi. Zan hallaka shi daga fuskar duniya, duk da haka ba zan hallaka gidan Yaƙub ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji.
Behold, the eyes of the Lord God are on the sinning kingdom, and I will wipe it from the face of the earth. Though truly, when destroying, I will not wipe away the house of Jacob, says the Lord.
9 “Gama zan ba da umarni, zan kuma tankaɗe gidan Isra’ila a cikin dukan ƙasashe kamar yadda ake tankaɗe hatsi a cikin matankaɗi kuma ko ƙwaya ɗaya ba za tă fāɗi a ƙasa ba.
For behold, I will command, and I will sift the house of Israel among all the nations, as wheat is sifted in a sieve. And not even one small stone will fall to the ground.
10 Dukan masu zunubi a cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, wato, su masu cewa, ‘Masifa ba za tă fāɗo ko ta same mu ba.’
All the sinners of my people will die by the sword. They say, “Disaster will not come near us, and it will not overcome us.”
11 “A wannan rana zan maido da tentin Dawuda da ya fāɗi. Zan gyaggyara wuraren da suka yayyage, in kuma maido da kufansa in gina shi kamar yadda yake a dā,
In that day, I will raise up the tabernacle of David, which is fallen. And I will repair the breaches in its walls, and I will restore that which collapsed. And I will rebuild it, just as in the days of antiquity,
12 domin su mallaki raguwar Edom da duk al’ummai da suke amsa sunana,” in ji Ubangiji shi wanda zai yi waɗannan abubuwa.
so that they may possess the remnant of Idumea and all the nations, for my name has been invoked over them, says the Lord who does this.
13 “Ranaku suna zuwa, in ji Ubangiji, “sa’ad da mai huɗa zai sha gaban mai girbi mai shuki kuma yă bi bayan mai matsin inabi. Sabon ruwan inabi zai ɗiga daga duwatsu yă kuma kwararo daga tuddai.
Behold, the days pass, says the Lord, and the plower will overtake the harvester, and the treader of grapes will overtake the sower of seed. And the mountains will drip sweetness, and every hill will be cultivated.
14 Zan dawo da waɗanda aka kai zaman bauta mutanena Isra’ila. “Za su sāke gina biranen da suke kango su kuma zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi su kuma sha ruwan inabinsu; za su yi lambuna su kuma ci amfaninsu.
And I will turn back the captivity of my people Israel. And they will rebuild the deserted cities and inhabit them. And they will plant vineyards and drink their wine. And they will create gardens and eat their fruits.
15 Zan dasa Isra’ila a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumɓuke su daga ƙasar da na ba su ba,” in ji Ubangiji Allahnku.
And I will plant them on their own soil. And I will no longer root them out of their own land, which I have given them, says the Lord your God.

< Amos 9 >