< Amos 9 >

1 Na ga Ubangiji yana tsaye a gaban bagade, ya kuma ce, “Bugi kan ginshiƙan don madogaran ƙofa su girgiza. Saukar da su a kan dukan mutane; waɗanda ba su mutu ba zan kashe su da takobi. Ba mutum guda da zai tsere, babu wani da zai tsira.
Viděl jsem Pána, an se postavil na oltáři a řekl: Udeř v makovici, až se zatřesou ty veřeje, a rozetni je všecky od vrchu jejich, ostatek pak mečem zmorduji. Neutečeť žádný z nich, aniž kdo z nich bude, ješto by toho znikl.
2 Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari, daga can hannuna zai fitar da su. Ko da sun hau can sama daga can zan sauko da su. (Sheol h7585)
Byť se pak do země zakopali, i odtud by je ruka má vzala; pakli by vstoupili do nebe, i odtud bych je strhl. (Sheol h7585)
3 Ko da sun ɓuya a bisa Karmel, a can zan farauce su in cafko. Ko da sun ɓuya can ƙarƙashin teku, a can zan umarci maciji yă sare su.
A jestliže by se schovali na vrchu Karmele, vyhledám a vezmu je odtud; pakli by se skryli před očima mýma na dně moře, přikáži hadu, aby je i odtud vyhryzl.
4 Ko da abokan gābansu sun kore su zuwa zaman bauta, a can zan umarci takobi yă kashe su. “Zan sa musu ido don mugunta ba don alheri ba.”
Pakliť by šli v zajetí před nepřátely svými, i tam přikáži meči, aby je zmordoval; obrátím zajisté oko své proti nim k zlému, a ne k dobrému.
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, shi da yakan taɓa ƙasa sai ta narke, kuma dukan mazauna cikinta suna makoki, ƙasar gaba ɗaya takan hau ta kuma sauka kamar Nilu, sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar,
Nebo Panovník Hospodin zástupů když se jen dotkne země, rozplývá se, a kvílí všickni přebývající na ní, a vystupuje všecka jako potok, a zatopena bývá jako potokem Egyptským,
6 shi da ya gina kyakkyawar fadarsa a cikin sammai ya kuma kafa harsashenta a duniya, shi da yakan kira ruwan teku yă kuma kwarara su a bisa duniya, Ubangiji ne sunansa.
Kterýž vzdělal na nebesích paláce své, a zástup svůj na zemi sšikoval, kterýž může zavolati vody mořské, a vyliti ji na svrchek země, jehož jméno jest Hospodin.
7 “Ku ba Isra’ilawa ba ne, daidai gare ni kamar yadda Kushawa suke?” In ji Ubangiji. “Ban fito da Isra’ila daga Masar ba, Filistiyawa kuma daga Kaftor Arameyawa kuma daga Kir ba?
Zdaliž nejste podobni synům Mouřenínů přede mnou, ó synové Izraelovi? dí Hospodin. Zdaliž jsem Izraele nevyvedl z země Egyptské, tak jako Filistinské z Kaftor, a Syrské z Kir?
8 “Tabbatacce idanun Ubangiji Mai Iko Duka suna a kan mulkin nan mai zunubi. Zan hallaka shi daga fuskar duniya, duk da haka ba zan hallaka gidan Yaƙub ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji.
Aj, oči Panovníka Hospodina proti království tomuto hřešícímu, abych je vyhladil se svrchku země, a však nevyhladím docela domu Jákobova, dí Hospodin.
9 “Gama zan ba da umarni, zan kuma tankaɗe gidan Isra’ila a cikin dukan ƙasashe kamar yadda ake tankaɗe hatsi a cikin matankaɗi kuma ko ƙwaya ɗaya ba za tă fāɗi a ƙasa ba.
Nebo aj, já přikázal jsem, a budu zmítati domem Izraelským mezi všemi národy, tak jako zmítáno bývá na říčici, tak že ani kameníčko nepropadne na zem.
10 Dukan masu zunubi a cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, wato, su masu cewa, ‘Masifa ba za tă fāɗo ko ta same mu ba.’
Mečem zbiti budou všickni hříšníci z lidu mého, kteříž říkají: Nepřiblížíť se, aniž potká nás to zlé.
11 “A wannan rana zan maido da tentin Dawuda da ya fāɗi. Zan gyaggyara wuraren da suka yayyage, in kuma maido da kufansa in gina shi kamar yadda yake a dā,
V ten den zdvihnu stánek Davidův, kterýž klesá, a zahradím mezery jeho, a zbořeniny jeho opravím, a vzdělám jej jako za dnů starodávních,
12 domin su mallaki raguwar Edom da duk al’ummai da suke amsa sunana,” in ji Ubangiji shi wanda zai yi waɗannan abubuwa.
Aby dědili s ostatky Idumejských a se všechněmi národy, nad kterýmiž jest vzýváno jméno mé, dí Hospodin, kterýž to učiní.
13 “Ranaku suna zuwa, in ji Ubangiji, “sa’ad da mai huɗa zai sha gaban mai girbi mai shuki kuma yă bi bayan mai matsin inabi. Sabon ruwan inabi zai ɗiga daga duwatsu yă kuma kwararo daga tuddai.
Aj, dnové jdou, dí Hospodin, že postihati bude oráč žence, a ten, kdož tlačí hrozny, rozsevače, hory pak dštíti budou mstem, a všickni pahrbkové oplývati.
14 Zan dawo da waɗanda aka kai zaman bauta mutanena Isra’ila. “Za su sāke gina biranen da suke kango su kuma zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi su kuma sha ruwan inabinsu; za su yi lambuna su kuma ci amfaninsu.
Přivedu také zase zajatý lid svůj Izraelský, a vystavějí města zpuštěná, aby v nich bydlili; a budou štěpovati vinice, a píti víno jejich, nadělají i zahrad, a jísti budou ovoce jejich.
15 Zan dasa Isra’ila a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumɓuke su daga ƙasar da na ba su ba,” in ji Ubangiji Allahnku.
A tak je štípím v zemi jejich, že nebudou vykořeněni více z země své, kterouž jsem dal jim, praví Hospodin Bůh tvůj.

< Amos 9 >