< Amos 8 >

1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji ya nuna mini kwandon nunannun’ya’yan itace.
Egemen RAB bana şunu gösterdi: Baktım bir sepet olgun meyve.
2 Ya yi tambaya ya ce, “Me ka gani Amos?” Sai na amsa na ce, “Kwandon nunannun’ya’yan itace.” Sai Ubangiji ya ce mini, “Lokaci ya yi wa mutanena Isra’ila da ba zan ƙara barinsu ba.
Bana, “Ne görüyorsun, Amos?” diye sordu. “Bir sepet olgun meyve” diye yanıtladım. Bunun üzerine RAB, “Halkım İsrail'in sonu geldi” dedi, “Bir daha onları esirgemeyeceğim.
3 “A ranan nan,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “Waƙoƙin a haikali za su koma makoki. Za a ga gawawwaki a ko’ina! Shiru!”
O gün saraydaki türküler yas çığlıklarına dönecek.” Egemen RAB, “Her yer atılmış cesetlerle dolacak, sessizlik hüküm sürecek” diyor.
4 Ku ji wannan, ku da kuke tattake masu bukata kuka kori matalautan ƙasar.
Dinleyin bunu, ey yoksulu çiğneyenler, Ülkedeki mazlumları yok edenler!
5 Kuna cewa, “Yaushe Sabon Wata zai wuce don mu sayar da hatsi, Asabbaci ta wuce, don mu sayar da alkama?” Mu yi awo da ma’aunin zalunci mu ƙara kuɗin kaya mu kuma cutar da mai saya,
Diyorsunuz ki, “Yeni Ay Töreni geçse de tahılımızı satsak, Şabat Günü geçse de buğdayımızı satışa çıkarsak. Ölçeği küçültüp fiyatı yükseltsek, Hileli tartı kullanıp
6 mu sayi matalauta da azurfa masu bukata kuma da takalmi, mu sayar da alkamar haɗe da yayi.
Yoksulları gümüş, Mazlumları bir çift çarık karşılığında satın alsak. Buğday yerine süprüntüsünü satsak.”
7 Ubangiji ya rantse da Girman Yaƙub, “Ba zan taɓa mantawa da duk wani abin da suka yi ba.
Yakup soyunun gurur duyduğu RAB kendi başı üstüne ant içti: “Onların yaptıklarının hiçbirini asla unutmayacağım.
8 “Shin, ƙasar ba za tă yi rawan jiki saboda wannan ba, kuma duk masu zama a cikinta ba za su yi makoki ba? Ƙasar duka za tă hau ta sauka kamar Nilu; za a dama ta sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar.
Bu yüzden yer sarsılmayacak mı, Üzerinde yaşayan herkes yas tutmayacak mı? Bütün yer Nil gibi yükselecek, Kabarıp yine inecek Mısır'ın ırmağı gibi.”
9 “A wannan rana,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “Zan sa rana ta fāɗi da tsakar rana in kuma duhunta duniya da rana tsaka.
“O gün” diyor Egemen RAB, “Öğleyin güneşi batıracağım, Güpegündüz yeryüzünü karartacağım.
10 Zan mai da bukukkuwanku na addini su zama makoki kuma dukan waƙoƙinku su zama kuka. Zan sa dukanku ku sa rigunan makoki za ku kuma aske kawunanku. Zan sa wannan lokaci yă zama kamar lokacin da ake makokin ɗan tilon da ake da shi kuma ƙarshenta kamar rana mai ɗaci.
Bayramlarınızı yasa, Bütün ezgilerinizi ağıta döndüreceğim. Her bele çul kuşattıracağım, Her başın saçını yoldurtacağım. O günü biricik oğulun ardından tutulan yasa çevirecek, Sonunu acı getireceğim.
11 “Ranakun suna zuwa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “sa’ad da zan aika da yunwa cikin ƙasar, ba yunwar abinci ko ta ƙishirwa ba, sai dai yunwa ta jin maganar Ubangiji.
“İşte günler geliyor, Ülkeye kıtlık göndereceğim” Diyor Egemen RAB, “Ekmek ya da su kıtlığı değil, RAB'bin sözlerine susamışlık göndereceğim.
12 Mutane za su yi ta tangaɗi daga teku zuwa teku suna yawo daga arewa zuwa kudu, suna neman maganar Ubangiji, amma ba za su samu ba.
RAB'bin sözünü bulmak için İnsanlar denizden denize, Kuzeyden doğuya dek dolaşacak, Oraya buraya koşacak, ama bulamayacaklar.
13 “A wannan rana “kyawawan’yan mata da kuma samari masu ji da ƙarfi za su suma don ƙishirwa.
O gün güzel kızlar, Yiğitler susuzluktan bayılacak.
14 Waɗanda suka yi rantsuwa da abin kunya na Samariya, ko kuma su ce, ‘Muddin allahnku yana a raye, ya Dan,’ ko kuwa, ‘Muddin allahn Beyersheba yana a raye,’ za su fāɗi, ba kuwa za su ƙara tashi ba.”
Samiriye tanrıçası Aşima üzerine ant içenler, ‘Ey Dan, senin ilahının başı üzerine’ Ve, ‘Beer-Şeva ilahının başı üzerine’ diyenler Düşecek ve bir daha kalkmayacak.”

< Amos 8 >