< Amos 8 >
1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji ya nuna mini kwandon nunannun’ya’yan itace.
O Senhor Jehovah assim me mostrou: e eis aqui um cesto de fructos do verão.
2 Ya yi tambaya ya ce, “Me ka gani Amos?” Sai na amsa na ce, “Kwandon nunannun’ya’yan itace.” Sai Ubangiji ya ce mini, “Lokaci ya yi wa mutanena Isra’ila da ba zan ƙara barinsu ba.
E disse: Que vês, Amós? E eu disse: Um cesto de fructos do verão. Então o Senhor me disse: Tem vindo o fim sobre o meu povo Israel; d'aqui por diante nunca mais passarei por elle.
3 “A ranan nan,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “Waƙoƙin a haikali za su koma makoki. Za a ga gawawwaki a ko’ina! Shiru!”
Mas os canticos do templo serão ouvidos n'aquelle dia, diz o Senhor Jehovah: multiplicar-se-hão os cadaveres, em todos os logares, serão lançados fóra em silencio.
4 Ku ji wannan, ku da kuke tattake masu bukata kuka kori matalautan ƙasar.
Ouvi isto, vós que anhelaes o abatimento do necessitado; e isto para destruirdes os miseraveis da terra:
5 Kuna cewa, “Yaushe Sabon Wata zai wuce don mu sayar da hatsi, Asabbaci ta wuce, don mu sayar da alkama?” Mu yi awo da ma’aunin zalunci mu ƙara kuɗin kaya mu kuma cutar da mai saya,
Dizendo: Quando passará a lua nova, para vendermos o grão? e o sabbado, para abrirmos os celleiros de trigo? diminuindo o epha, e augmentando o siclo, e falsificando as balanças enganosas;
6 mu sayi matalauta da azurfa masu bukata kuma da takalmi, mu sayar da alkamar haɗe da yayi.
Para comprarmos os pobres por dinheiro, e os necessitados por um par de sapatos? então venderemos as cascas do trigo.
7 Ubangiji ya rantse da Girman Yaƙub, “Ba zan taɓa mantawa da duk wani abin da suka yi ba.
Jurou o Senhor pela gloria de Jacob: Eu me não esquecerei de todas as suas obras para sempre.
8 “Shin, ƙasar ba za tă yi rawan jiki saboda wannan ba, kuma duk masu zama a cikinta ba za su yi makoki ba? Ƙasar duka za tă hau ta sauka kamar Nilu; za a dama ta sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar.
Por causa d'isto não se commoveria a terra? e não choraria todo aquelle que habita n'ella? certamente levantar-se-ha toda como um rio, e será arrojada, e será fundida como pelo rio do Egypto.
9 “A wannan rana,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “Zan sa rana ta fāɗi da tsakar rana in kuma duhunta duniya da rana tsaka.
E succederá que, n'aquelle dia, diz o Senhor, farei que o sol se ponha ao meio dia, e a terra se entenebreça no dia da luz.
10 Zan mai da bukukkuwanku na addini su zama makoki kuma dukan waƙoƙinku su zama kuka. Zan sa dukanku ku sa rigunan makoki za ku kuma aske kawunanku. Zan sa wannan lokaci yă zama kamar lokacin da ake makokin ɗan tilon da ake da shi kuma ƙarshenta kamar rana mai ɗaci.
E tornarei as vossas festas em luto, e todos os vossos canticos em lamentações, e farei pôr sacco sobre todos os lombos, e calva sobre toda a cabeça; e farei que isso seja como luto do filho unico, e o seu fim como dia de amarguras.
11 “Ranakun suna zuwa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “sa’ad da zan aika da yunwa cikin ƙasar, ba yunwar abinci ko ta ƙishirwa ba, sai dai yunwa ta jin maganar Ubangiji.
Eis que veem dias, diz o Senhor Jehovah, em que enviarei fome sobre a terra, não fome de pão, nem sêde de agua, mas de ouvir as palavras do Senhor.
12 Mutane za su yi ta tangaɗi daga teku zuwa teku suna yawo daga arewa zuwa kudu, suna neman maganar Ubangiji, amma ba za su samu ba.
E irão vagabundos de um mar até outro mar, e do norte até ao oriente: correrão por toda a parte, buscando a palavra do Senhor, mas não a acharão.
13 “A wannan rana “kyawawan’yan mata da kuma samari masu ji da ƙarfi za su suma don ƙishirwa.
N'aquelle dia as virgens formosas e os mancebos desmaiarão á sêde.
14 Waɗanda suka yi rantsuwa da abin kunya na Samariya, ko kuma su ce, ‘Muddin allahnku yana a raye, ya Dan,’ ko kuwa, ‘Muddin allahn Beyersheba yana a raye,’ za su fāɗi, ba kuwa za su ƙara tashi ba.”
Os que juram pelo delicto de Samaria, e dizem: Vive o teu deus, ó Dan, e: Vive o caminho de Berseba; e cairão, e não se levantarão mais.