< Amos 8 >

1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji ya nuna mini kwandon nunannun’ya’yan itace.
خداوند یهوه به من چنین نمودار ساخت واینک سبدی پر از میوه‌ها.۱
2 Ya yi tambaya ya ce, “Me ka gani Amos?” Sai na amsa na ce, “Kwandon nunannun’ya’yan itace.” Sai Ubangiji ya ce mini, “Lokaci ya yi wa mutanena Isra’ila da ba zan ƙara barinsu ba.
و گفت: «ای عاموس چه می‌بینی؟» من جواب دادم که «سبدی از میوه.» و خداوند به من گفت: «انتها بر قوم من اسرائیل رسیده است و از ایشان دیگر درنخواهم گذشت.»۲
3 “A ranan nan,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “Waƙoƙin a haikali za su koma makoki. Za a ga gawawwaki a ko’ina! Shiru!”
خداوند یهوه می‌گوید که در آن روزسرودهای هیکل به ولوله مبدل خواهد شد ولاشهای بسیار خواهد بود و آنها را در هر جا به خاموشی بیرون خواهند انداخت.۳
4 Ku ji wannan, ku da kuke tattake masu bukata kuka kori matalautan ƙasar.
‌ای شما که می‌خواهید فقیران را ببلعید ومسکینان زمین را هلاک کنید این را بشنوید.۴
5 Kuna cewa, “Yaushe Sabon Wata zai wuce don mu sayar da hatsi, Asabbaci ta wuce, don mu sayar da alkama?” Mu yi awo da ma’aunin zalunci mu ƙara kuɗin kaya mu kuma cutar da mai saya,
ومی گویید که غره ماه کی خواهد گذشت تا غله رابفروشیم و روز سبت تا انبارهای گندم را بگشاییم و ایفا را کوچک و مثقال را بزرگ ساخته، میزانهارا قلب و معوج نماییم.۵
6 mu sayi matalauta da azurfa masu bukata kuma da takalmi, mu sayar da alkamar haɗe da yayi.
و مسکینان را به نقره و فقیران را به نعلین بخریم و پس مانده گندم رابفروشیم.۶
7 Ubangiji ya rantse da Girman Yaƙub, “Ba zan taɓa mantawa da duk wani abin da suka yi ba.
خداوند به جلال یعقوب قسم خورده است که هیچکدام از اعمال ایشان را هرگزفراموش نخواهم کرد.۷
8 “Shin, ƙasar ba za tă yi rawan jiki saboda wannan ba, kuma duk masu zama a cikinta ba za su yi makoki ba? Ƙasar duka za tă hau ta sauka kamar Nilu; za a dama ta sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar.
آیا به این سبب زمین متزلزل نخواهد شد و همه ساکنانش ماتم نخواهند گرفت و تمامش مثل نهر برنخواهد آمدو مثل نیل مصر سیلان نخواهد کرد و فرو نخواهدنشست.۸
9 “A wannan rana,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “Zan sa rana ta fāɗi da tsakar rana in kuma duhunta duniya da rana tsaka.
و خداوند یهوه می‌گوید: «که در آن روزآفتاب را در وقت ظهر فرو خواهم برد و زمین رادر روز روشن تاریک خواهم نمود.۹
10 Zan mai da bukukkuwanku na addini su zama makoki kuma dukan waƙoƙinku su zama kuka. Zan sa dukanku ku sa rigunan makoki za ku kuma aske kawunanku. Zan sa wannan lokaci yă zama kamar lokacin da ake makokin ɗan tilon da ake da shi kuma ƙarshenta kamar rana mai ɗaci.
و عیدهای شما را به ماتم و همه سرودهای شما را به مرثیه هامبدل خواهم ساخت. و بر هر کمر پلاس و بر هرسر گری برخواهم آورد و آن را مثل ماتم پسریگانه و آخرش را مانند روز تلخی خواهم گردانید.»۱۰
11 “Ranakun suna zuwa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “sa’ad da zan aika da yunwa cikin ƙasar, ba yunwar abinci ko ta ƙishirwa ba, sai dai yunwa ta jin maganar Ubangiji.
اینک خداوند یهوه می‌گوید: «ایامی می‌آید که گرسنگی بر زمین خواهم فرستاد نه گرسنگی از نان و نه تشنگی از آب بلکه از شنیدن کلام خداوند.۱۱
12 Mutane za su yi ta tangaɗi daga teku zuwa teku suna yawo daga arewa zuwa kudu, suna neman maganar Ubangiji, amma ba za su samu ba.
و ایشان از دریا تا دریا و ازشمال تا مشرق پراکنده خواهند شد و گردش خواهند کرد تا کلام خداوند را بطلبند اما آن رانخواهند یافت.۱۲
13 “A wannan rana “kyawawan’yan mata da kuma samari masu ji da ƙarfi za su suma don ƙishirwa.
در آن روز دوشیزگان جمیل وجوانان از تشنگی ضعف خواهند کرد.۱۳
14 Waɗanda suka yi rantsuwa da abin kunya na Samariya, ko kuma su ce, ‘Muddin allahnku yana a raye, ya Dan,’ ko kuwa, ‘Muddin allahn Beyersheba yana a raye,’ za su fāɗi, ba kuwa za su ƙara tashi ba.”
آنانی که به گناه سامره قسم خورده، می‌گویند که «ای دان به حیات خدای تو و به طریقت بئرشبع قسم می‌خوریم»، خواهند افتاد و بار دیگر نخواهندبرخاست.۱۴

< Amos 8 >