< Amos 8 >
1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji ya nuna mini kwandon nunannun’ya’yan itace.
Voici ce que m’a montré le Seigneur Dieu; or voici un crochet pour abattre des fruits.
2 Ya yi tambaya ya ce, “Me ka gani Amos?” Sai na amsa na ce, “Kwandon nunannun’ya’yan itace.” Sai Ubangiji ya ce mini, “Lokaci ya yi wa mutanena Isra’ila da ba zan ƙara barinsu ba.
Et il dit: Que vois-tu, Amos? Et je dis: Un crochet pour abattre des fruits. Et le Seigneur me dit: Elle est venue, la fin pour mon peuple d’Israël; je ne le traverserai plus à l’avenir.
3 “A ranan nan,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “Waƙoƙin a haikali za su koma makoki. Za a ga gawawwaki a ko’ina! Shiru!”
Et les gonds du temple retentiront en ce jour-là, dit le Seigneur Dieu; beaucoup mourront; en tout lieu régnera le silence.
4 Ku ji wannan, ku da kuke tattake masu bukata kuka kori matalautan ƙasar.
Ecoutez ceci, vous qui écrasez le pauvre, et qui faites défaillir les indigents de la terre,
5 Kuna cewa, “Yaushe Sabon Wata zai wuce don mu sayar da hatsi, Asabbaci ta wuce, don mu sayar da alkama?” Mu yi awo da ma’aunin zalunci mu ƙara kuɗin kaya mu kuma cutar da mai saya,
Disant: Quand sera passé le mois, alors nous vendrons nos marchandises; et quand sera passé le Sabbat, alors nous ouvrirons nos greniers de blé, afin que nous diminuions la mesure, et que nous augmentions le sicle, et que nous substituions des balances trompeuses,
6 mu sayi matalauta da azurfa masu bukata kuma da takalmi, mu sayar da alkamar haɗe da yayi.
Afin d’avoir en notre possession, pour de l’argent, des indigents et des pauvres, pour des chaussures, et que nous vendions le rebut du blé.
7 Ubangiji ya rantse da Girman Yaƙub, “Ba zan taɓa mantawa da duk wani abin da suka yi ba.
Le Seigneur a juré contre l’orgueil de Jacob: Si j’oublierai jamais aucune de leurs œuvres.
8 “Shin, ƙasar ba za tă yi rawan jiki saboda wannan ba, kuma duk masu zama a cikinta ba za su yi makoki ba? Ƙasar duka za tă hau ta sauka kamar Nilu; za a dama ta sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar.
Est-ce que sur cela la terre ne sera pas ébranlée, et que tous ses habitants ne seront pas dans le deuil? et que tous entièrement ne monteront pas comme le fleuve, et qu’ils ne seront pas chassés, et qu’ils ne s’écouleront pas comme le fleuve d’Egypte?
9 “A wannan rana,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “Zan sa rana ta fāɗi da tsakar rana in kuma duhunta duniya da rana tsaka.
Et il arrivera en ce jour-là, dit le Seigneur Dieu, que le soleil se couchera à midi, et je ferai que la terre se couvrira de ténèbres en un jour de lumière.
10 Zan mai da bukukkuwanku na addini su zama makoki kuma dukan waƙoƙinku su zama kuka. Zan sa dukanku ku sa rigunan makoki za ku kuma aske kawunanku. Zan sa wannan lokaci yă zama kamar lokacin da ake makokin ɗan tilon da ake da shi kuma ƙarshenta kamar rana mai ɗaci.
Et je convertirai vos fêtes en deuil, et tous vos cantiques en lamentations; et je mettrai sur tous vos reins un cilice, et sur toutes vos têtes la calvitie; et je plongerai Israël dans le deuil, comme à la mort d’un fils unique, et ses derniers moments seront comme un jour amer.
11 “Ranakun suna zuwa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka, “sa’ad da zan aika da yunwa cikin ƙasar, ba yunwar abinci ko ta ƙishirwa ba, sai dai yunwa ta jin maganar Ubangiji.
Voilà que des jours viennent, dit le Seigneur, et j’enverrai la faim sur la terre, non la faim du pain, ni la soif de l’eau, mais d’entendre la parole du Seigneur.
12 Mutane za su yi ta tangaɗi daga teku zuwa teku suna yawo daga arewa zuwa kudu, suna neman maganar Ubangiji, amma ba za su samu ba.
Et ils seront dans le trouble depuis une mer jusqu’à l’autre, et depuis l’aquilon jusqu’à l’orient; ils iront de tous côtés, cherchant la parole du Seigneur, et ils ne la trouveront pas.
13 “A wannan rana “kyawawan’yan mata da kuma samari masu ji da ƙarfi za su suma don ƙishirwa.
En ce jour-là, les vierges dans leur beauté et les jeunes hommes défaudront par la soif.
14 Waɗanda suka yi rantsuwa da abin kunya na Samariya, ko kuma su ce, ‘Muddin allahnku yana a raye, ya Dan,’ ko kuwa, ‘Muddin allahn Beyersheba yana a raye,’ za su fāɗi, ba kuwa za su ƙara tashi ba.”
Ceux qui jurent par le péché de Samarie et disent: Il vit, ton Dieu, Dan! et elle vit, la voie de Bersabée! tomberont et ne se relèveront plus.