< Amos 7 >
1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
Ово ми показа Господ Господ: Гле, саздаваше скакавце, кад почињаше ницати отава, и гле, беше отава по царевој косидби.
2 Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
А кад поједоше траву земаљску, тада рекох: Господе, Господе, смилуј се; како ће се подигнути Јаков? Јер је мали.
3 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
Господ се раскаја зато: Неће бити, рече Господ.
4 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
Тада ми показа Господ Господ, и гле, Господ Господ повика да ће судити огњем; и огањ прождре велику бездану и прождре део земље.
5 Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
А ја рекох: Господе, Господе, престани; како ће се подигнути Јаков? Јер је мали.
6 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Господ се раскаја зато: Ни то неће бити, рече Господ Господ.
7 Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
Тада ми показа, и гле, Господ стајаше на зиду сазиданом по мерилима, и у руци Му беху мерила.
8 Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
И рече ми Господ: Шта видиш, Амосе? И рекох: Мерила. А Господ ми рече: Ево, ја ћу метнути мерила посред народа свог Израиља, нећу га више пролазити.
9 “Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
Јер ће се разорити висине Исакове, и светиње ће Израиљеве опустети, и устаћу на дом Јеровоамов с мачем.
10 Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
Тада Амасија свештеник ветиљски посла к Јеровоаму цару Израиљевом и поручи му: Амос диже буну на те усред дома Израиљевог, земља не може поднети све речи његове.
11 Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
Јер овако говори Амос: Јеровоам ће погинути од мача, а Израиљ ће се одвести из земље своје у ропство.
12 Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
Потом рече Амасија Амосу: Видеоче, иди, бежи у земљу Јудину, и онде једи хлеб и онде пророкуј;
13 Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
А у Ветиљу више не пророкуј, јер је светиња царева и дом је царски.
14 Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
А Амос одговори и рече Амасији: Не бејах пророк ни пророчки син, него бех говедар и брах дудове;
15 Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
А Господ ме узе од стада и рече ми Господ: Иди, пророкуј народу мом Израиљу.
16 Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
Сада дакле чуј реч Господњу. Ти кажеш: Не пророкуј у Израиљу, и не кропи по дому Исаковом.
17 “Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
Зато овако вели Господ: Жена ће ти се курвати у граду, и синови ће твоји и кћери твоје пасти од мача, и земља ће се твоја разделити ужем, и ти ћеш умрети у нечистој земљи, а Израиљ ће се одвести из своје земље у ропство.