< Amos 7 >

1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
Assim o Senhor Javé me mostrou: eis que ele formou gafanhotos no início do crescimento deste último; e eis que foi este último crescimento após a colheita do rei.
2 Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
Quando terminaram de comer a erva da terra, então eu disse: “Senhor Javé, perdoa, eu te imploro! Como poderia Jacó resistir? Pois ele é pequeno”.
3 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
Yahweh cedeu a esse respeito. “Não será”, diz Yahweh.
4 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
Assim o Senhor Javé me mostrou: eis que o Senhor Javé pediu o julgamento pelo fogo; e ele secou a grande profundidade, e teria devorado a terra.
5 Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
Então eu disse: “Senhor Yahweh, pare, eu lhe imploro! Como poderia Jacó resistir? Pois ele é pequeno”.
6 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Yahweh cedeu a este respeito. “Isto também não será”, diz o Senhor Javé.
7 Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
Assim ele me mostrou: eis que o Senhor estava ao lado de uma parede feita por uma linha de prumo, com uma linha de prumo em sua mão.
8 Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
Yahweh me disse: “Amos, o que você vê?”. Eu disse: “Uma linha de prumo”. Então o Senhor disse: “Eis que porei uma linha de prumo no meio do meu povo Israel. Não passarei mais por eles”.
9 “Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
Os lugares altos de Isaac serão desolados, os santuários de Israel serão assolados; e me levantarei contra a casa de Jeroboão com a espada”.
10 Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
Então Amaziah o sacerdote de Betel enviou a Jeroboão, rei de Israel, dizendo: “Amós conspirou contra você no meio da casa de Israel”. A terra não é capaz de suportar todas as suas palavras.
11 Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
Pois Amós diz: 'Jeroboão morrerá pela espada, e Israel certamente será levado cativo para fora de sua terra'”.
12 Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
Amaziah também disse a Amós: “Vós, vidente, ide, fugi para a terra de Judá, e lá comei pão, e profetizai lá,
13 Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
mas não profetizeis mais em Betel; pois é o santuário do rei, e é uma casa real”!
14 Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
Então Amós respondeu ao Amazonas: “Eu não era profeta, nem filho de profeta, mas era um pastor e um fazendeiro de figos sicômoros;
15 Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
e Javé me tirou de seguir o rebanho, e Javé me disse: 'Vai, profetiza ao meu povo Israel'.
16 Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
Agora, portanto, escute a palavra de Javé: 'Não profetize contra Israel, e não pregue contra a casa de Isaac'.
17 “Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
Portanto, Javé diz: 'Sua mulher será prostituta na cidade, e seus filhos e suas filhas cairão à espada, e sua terra será dividida por linha; e você mesmo morrerá numa terra impura, e Israel certamente será levado cativo para fora de sua terra'”.

< Amos 7 >