< Amos 7 >
1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
Tas Kungs Dievs man šādu lietu lika redzēt, un redzi, Viņš rādīja siseņus, kad atāls sāka augt, un redzi, atāls bija audzis pēc ķēniņa pļaušanas.
2 Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
Un kad tie zāli zemes virsū visnotaļ bija aprijuši, tad es sacīju: Kungs Dievs, piedod jel! Kā Jēkabs varēs pastāvēt, jo viņš ir mazs.
3 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
Tad Tam Kungam bija žēl; tas nenotiks, sacīja Tas Kungs. -
4 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
Atkal Tas Kungs Dievs man šādu lietu lika redzēt, un redzi, Tas Kungs Dievs sauca un gribēja ar uguni sodīt, un tas jau norija to lielo jūru un aprija arī vienu zemes gabalu.
5 Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
Tad es sacīju: Kungs Dievs, mitējies jel! Kā Jēkabs varēs pastāvēt, jo viņš ir mazs.
6 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Tad tas Tam Kungam bija žēl; ir tas nenotiks, - sacīja Tas Kungs Dievs.
7 Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
Atkal viņš man šādu lietu lika redzēt, un redzi, Tas Kungs stāvēja uz stāva mūra, un lote(svina svērtenis) bija Viņa rokā.
8 Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
Un Tas Kungs sacīja uz mani: ko tu redzi, Amos? Tad es sacīju: loti. Tad Tas Kungs sacīja: redzi, Es pielikšu loti vidū Maniem Israēla ļaudīm, un viņus vairs netaupīšu;
9 “Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
Bet Īzaka elku kalni taps iznīcināti, un Israēla svētās vietas taps nopostītas, un Es celšos pret Jerobeama namu ar zobenu.
10 Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
Tad Amacīja, Bēteles priesteris, sūtīja pie Jerobeama, Israēla ķēniņa, un sacīja: Amos ceļ dumpi pret tevi Israēla nama vidū, zeme nevar panest visus viņa vārdus.
11 Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
Jo tā saka Amos: Jerobeams nomirs caur zobenu, un Israēls vešus no savas zemes taps aizvests.
12 Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
Un Amacīja sacīja uz Amosu: tu redzētāj, ej, bēdz uz Jūda zemi, un ēd tur savu maizi,
13 Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
Un sludini tur, bet Bētelē tev joprojām vairs nebūs sludināt, jo te ir ķēniņa svētā vieta, un te ir valsts pilsēta.
14 Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
Tad Amos atbildēja un sacīja uz Amacīju: es neesmu pravietis nedz pravieša dēls, bet es esmu lopu gans un lasu meža vīģes;
15 Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
Bet Tas Kungs mani ņēmis no ganāmā pulka, un Tas Kungs uz mani sacījis: ej, sludini Maniem Israēla ļaudīm.
16 Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
Nu tad, klausi Tā Kunga vārdu! Tu saki: nesludini pret Israēli un nemāci pret Īzaka namu.
17 “Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
Tādēļ, tā saka Tas Kungs: tava sieva pilsētā taps par mauku, un tavi dēli un tavas meitas kritīs caur zobenu, un tava zeme taps mērota un izdalīta, un tu mirsi nešķīstā zemē, un Israēls vešus no savas zemes taps aizvests.