< Amos 7 >

1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
Voici ce que m’a montré le Seigneur Dieu: or voici qu’il formait la sauterelle, lorsque les plantes commençaient à germer par la pluie de l’arrière-saison; et voici la pluie de l’arrière-saison après la coupe du roi.
2 Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
Et il arriva que lorsque la sauterelle eut achevé de manger l’herbe de la terre, je dis: Seigneur Dieu, soyez propice, je vous conjure; qui rétablira Jacob, car il est bien faible?
3 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
Sur cela, le Seigneur a eu pitié: Ce que tu crains ne sera pas, dit le Seigneur.
4 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
Voici ce que m’a montré le Seigneur Dieu; or, voici que le Seigneur Dieu appelait le feu pour exercer le jugement, et il dévora un grand abîme, et consuma en même temps une partie de la plaine.
5 Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
Et je dis: Seigneur Dieu, apaisez-vous, je vous conjure; qui rétablira Jacob, car il est bien faible?
6 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Sur cela, le Seigneur eut pitié: Il n’en sera pas ainsi, dit le Seigneur Dieu.
7 Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
Voici ce que m’a montré le Seigneur Dieu; voici que le Seigneur se tenait debout sur une muraille crépie, et que dans sa main était une truelle de maçon.
8 Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
Et le Seigneur me dit: Que vois-tu, Amos? Et je dis: Une truelle de maçon. Et le Seigneur dit: Voici que moi je déposerai la truelle au milieu de mon peuple d’Israël; et je ne le crépirai plus à l’avenir.
9 “Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
Et les hauts lieux consacrés à l’idole seront détruits, et les sanctuaires d’Israël seront désolés; et je m’élèverai avec le glaive contre la maison de Jéroboam.
10 Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
Et Amasias, prêtre de Béthel, envoya vers Jéroboam, roi d’Israël, disant: Amos s’est révolté contre toi au sein de la maison d’Israël. Ta terre ne pourra supporter tous ses discours.
11 Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
Car voici ce que dit Amos: Par le glaive mourra Jéroboam, et Israël émigrera de sa terre;
12 Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
Et Amasias dit à Amos: Toi qui vois, va, fuis dans la terre de Juda et mange là ton pain, et tu prophétiseras là.
13 Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
Mais dans Béthel tu ne prophétiseras plus à l’avenir, parce que c’est le sanctuaire du roi, et le siège du royaume.
14 Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
Et Amos répondit et dit à Amasias: Je ne suis pas fils de prophète, mais je suis pâtre, effeuillant des sycomores.
15 Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
Et le Seigneur m’a pris lorsque je suivais mon troupeau, et le Seigneur m’a dit: Va, prophétise à mon peuple d’Israël.
16 Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
Et maintenant écoute la parole du Seigneur: Tu dis: Tu ne prophétiseras pas sur Israël, et tu ne répandras pas tes oracles sur la maison de l’idole.
17 “Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur: Ta femme dans la cité forniquera; tes fils et tes filles sous le glaive tomberont; ton sol sera mesuré au cordeau; et toi, c’est sur une terre souillée que tu mourras, et Israël captif émigrera de sa terre.

< Amos 7 >