< Amos 7 >
1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
Tämän näytti minulle Herra, Herra: Katso, hän loi heinäsirkkoja, kun äpäreheinä alkoi nousta; ja katso, se oli äpäreheinä kuninkaan niitosten jälkeen.
2 Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
Ja kun ne olivat syöneet loppuun maan kasvit, sanoin minä: "Herra, Herra, anna anteeksi. Kuinka voi Jaakob pysyä, sillä hän on vähäinen?"
3 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
Niin Herra katui sitä. "Ei se ole tapahtuva", sanoi Herra.
4 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
Tämän näytti minulle Herra, Herra: Katso, Herra, Herra kutsui tulen toimittamaan tuomiota, ja se kulutti suuren syvyyden, ja se kulutti peltomaan.
5 Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
Niin minä sanoin: "Herra, Herra, lakkaa jo. Kuinka voi Jaakob pysyä, sillä hän on vähäinen?"
6 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Niin Herra katui sitä. "Ei sekään ole tapahtuva", sanoi Herra, Herra.
7 Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
Tämän hän näytti minulle: Katso, Herra seisoi pystysuoralla muurilla, kädessänsä luotilanka.
8 Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
Ja Herra sanoi minulle: "Mitä sinä näet, Aamos?" Minä vastasin: "Luotilangan". Ja Herra sanoi minulle: "Katso, minä olen laskenut luotilangan kansani Israelin keskelle. Minä en enää mene säästäen sen ohitse,
9 “Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
vaan Iisakin uhrikukkulat tulevat autioiksi ja Israelin pyhäköt raunioiksi. Ja minä nousen ja nostan miekan Jerobeamin sukua vastaan."
10 Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
Silloin Amasja, Beetelin pappi, lähetti Jerobeamille, Israelin kuninkaalle, tämän sanan: "Aamos on tehnyt salaliiton sinua vastaan Israelin heimon keskuudessa. Ei maa kestä kaikkea, mitä hän puhuu.
11 Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
Sillä näin on Aamos sanonut: 'Jerobeam kuolee miekkaan, ja Israel viedään pakkosiirtolaisuuteen, pois omasta maastansa'."
12 Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
Ja Amasja sanoi Aamokselle: "Sinä näkijä, mene matkaasi ja pakene Juudan maahan, syö leipäsi siellä ja ennusta siellä.
13 Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
Mutta Beetelissä älä ennusta enää, sillä se on kuninkaan pyhäkkö ja valtakunnan temppeli."
14 Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
Niin Aamos vastasi ja sanoi Amasjalle: "En minä ole profeetta enkä profeetanoppilas, vaan minä olen paimen ja metsäviikunapuiden viljelijä.
15 Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
Ja Herra otti minut laumojeni äärestä, ja Herra sanoi minulle: 'Mene ja ennusta minun kansaani Israelia vastaan'.
16 Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
Kuule siis nyt Herran sana: Sinä sanot: 'Älä ennusta Israelia vastaan, äläkä saarnaa Iisakin heimoa vastaan'.
17 “Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
Sentähden, näin sanoo Herra: Sinun vaimosi joutuu portoksi kaupungissa, sinun poikasi ja tyttäresi kaatuvat miekkaan, sinun maasi jaetaan mittanuoralla, sinä itse kuolet saastaisessa maassa, ja Israel viedään pakkosiirtolaisuuteen, pois omasta maastansa."