< Amos 7 >

1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
The Lord God schewide these thingis to me; and lo! a makere of locust in bigynnyng of buriownynge thingis of euentid reyn, and lo! euentid reyn after the clippere of the kyng.
2 Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
And it was don, whanne he hadde endid for to ete the erbe of erthe, Y seide, Lord God, Y biseche, be thou merciful; who schal reise Jacob, for he is litil?
3 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
The Lord hadde merci on this thing; It schal not be, seide the Lord God.
4 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
The Lord God schewide to me these thingis; and lo! the Lord God schal clepe doom to fier, and it schal deuoure myche depthe of watir, and it eet togidere a part.
5 Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
And Y seide, Lord God, Y biseche, reste thou; who schal reise Jacob, for he is litil?
6 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
The Lord hadde merci on this thing; But and this thing schal not be, seide the Lord God.
7 Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
The Lord God schewide to me these thingis; and lo! the Lord stondinge on a wal plastrid, and in the hond of hym was a trulle of a masoun.
8 Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
And the Lord seide to me, What seest thou, Amos? And Y seide, A trulle of a masoun. And the Lord seide, Lo! I schal putte a trulle in the myddil of my puple Israel; Y schal no more putte to, for to ouerlede it;
9 “Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
and the hiy thingis of idol schulen be distried, and the halewyngis of Israel schulen be desolat; and Y schal rise on the hous of Jeroboam bi swerd.
10 Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
And Amasie, prest of Bethel, sente to Jeroboam, kyng of Israel, and seide, Amos rebellide ayens thee, in the myddil of the hous of Israel; the lond mai not susteyne alle hise wordis.
11 Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
For Amos seith these thingis, Jeroboam schal die bi swerd, and Israel caitif schal passe fro his lond.
12 Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
And Amasie seide to Amos, Thou that seest, go; fle thou in to the lond of Juda, and ete thou there thi breed; and there thou schalt profesie.
13 Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
And thou schalt no more put to, that thou profesie in Bethel, for it is the halewyng of the king, and is the hous of the rewme.
14 Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
And Amos answeride, and seide to Amasie, Y am not a profete, and Y am not sone of profete; but an herde of neet Y am, drawyng vp sicomoris.
15 Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
And the Lord took me, whanne Y suede the floc; and the Lord seide to me, Go, and profesie thou to my puple Israel.
16 Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
And now here thou the word of the Lord. Thou seist, Thou schalt not profesie on Israel, and thou schal not droppe on the hous of idol.
17 “Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
For this thing the Lord seith these thingis, Thi wijf schal do fornicacioun in the citee, and thi sones and thi douytris schal falle bi swerd, and thi lond schal be motun with a litil coord; and thou schalt die in a pollutid lond, and Israel caitif schal passe fro his lond.

< Amos 7 >