< Amos 7 >
1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
Thus he showed me [the] Lord Yahweh and there! [he was] forming locusts at [the] beginning of [the] coming up of the spring-crop and there! a spring-crop after [the] mowings of the king.
2 Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
And it will be if it had finished to eat [the] vegetation of the land and I said O Lord Yahweh forgive please who? will he stand Jacob for [is] small he.
3 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
He relented Yahweh on this not it will be he said Yahweh.
4 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
Thus he showed me [the] Lord Yahweh and there! [was] calling for conducting a case by fire [the] Lord Yahweh and it consumed [the] deep great and it consumed the portion of land.
5 Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
And I said O Lord Yahweh cease please who? will he stand Jacob for [is] small he.
6 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
He relented Yahweh on this also it not it will be he said [the] Lord Yahweh.
7 Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
Thus he showed me and there! [the] Lord [was] standing on a wall of tin and [was] in hand his tin.
8 Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
And he said Yahweh to me what? [are] you seeing O Amos and I said tin and he said [the] Lord here I [am] about to put tin in [the] midst of people my Israel not I will repeat again to pass by it.
9 “Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
And they will be made desolate [the] high places of Isaac and [the] sanctuaries of Israel they will be waste and I will arise on [the] house of Jeroboam with the sword.
10 Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
And he sent Amaziah [the] priest of Beth-el to Jeroboam [the] king of Israel saying he has conspired on you Amos in [the] midst of [the] house of Israel not it is able the land to endure all words his.
11 Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
For thus he has said Amos by the sword he will die Jeroboam and Israel certainly it will go into exile from on land its.
12 Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
And he said Amaziah to Amos O seer go flee yourself to [the] land of Judah and eat there bread and there you will prophesy.
13 Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
And Beth-el not you must repeat again to prophesy for [is] a sanctuary of a king it and [is] a house of kingdom it.
14 Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
And he answered Amos and he said to Amaziah not [am] a prophet I and not [am] a son of a prophet I for [was] a herdsman I and a fig picker of sycamores.
15 Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
And he took me Yahweh from after the flock and he said to me Yahweh go prophesy to people my Israel.
16 Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
And therefore hear [the] word of Yahweh you [are] saying not you must prophesy on Israel and not you must prophesy on [the] house of Isaac.
17 “Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
Therefore thus he says Yahweh wife your in the city she will be a prostitute and sons your and daughters your by the sword they will fall and land your with measuring-line it will be divided and you on ground unclean you will die and Israel certainly it will go into exile from on land its.