< Amos 7 >

1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
This is what the Lord God showed me: he was forming a swarm of locusts, when the late spring grass began to come up after the king’s share had been harvested.
2 Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
And when they had finished devouring all the land’s vegetation, I said: “Lord God, forgive, I beg you! How can Jacob survive, for he is so helpless?”
3 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
The Lord relented. This will not happen,” said the Lord.
4 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
This is what he showed me: the Lord God was giving command to execute judgment by fire. It burned up the great deep, and had begun to devour the fields, and I said:
5 Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
“Lord God, forgive, I beg you! How can Jacob survive, for he is so helpless?”
6 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
The Lord relented. “This will not happen either,” said the Lord.
7 Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
This is what the Lord God showed me: the Lord was standing beside a wall built with a plumb line, with a plumb line in his hand.
8 Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
And the Lord said to me, “What do you see, Amos?” And I answered, “A plumb line,” Then the Lord said, “Watch: I am setting a plumb line in the midst of my people Israel, I will no longer overlook their crookedness.
9 “Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
And the high places of Isaac will be desolate, the sanctuaries of Israel will be laid waste, and I will rise up against the house of Jeroboam with the sword.”
10 Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
Then Amaziah, chief priest of Bethel sent this message to King Jeroboam of Israel: “Amos has conspired against you right in the heart of Israel. The country cannot survive all his words.
11 Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
Amos has said, ‘Jeroboam will die by the sword, and Israel will be led away captive out of their land.’”
12 Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
And Amaziah said to Amos, “Leave, you who see visions, go to the land of Judah. Earn your bread there and prophesy there,
13 Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
but don’t prophesy any more at Bethel, for it is the king’s sanctuary, and it is the royal residence.”
14 Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
“I am no prophet,” Amos answered Amaziah, “nor trained as one. I am a shepherd and a keeper of sycamores fig trees.
15 Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
But the Lord took me away from following the flock, and the Lord said to me, ‘Go, prophesy to my people Israel.’
16 Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
Now therefore listen to the Lord’s message: ‘You say not to prophesy against Israel, nor to preach against the house of Isaac.
17 “Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
But the Lord says: Your wife will become a prostitute in the city, your sons and your daughters will fall by the sword, your land will be divided up, you will die on unclean soil, and Israel will be led away captive out of their land.’”

< Amos 7 >