< Amos 7 >

1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
Thus Lord YHWH has showed me, and behold, He is forming locusts at the beginning of the ascending of the latter growth, and behold, the latter growth [is] after the mowings of the king [[or King Gog]];
2 Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
and it has come to pass, when it has finished to consume the herb of the land, that I say, “Lord YHWH, please forgive, How does Jacob arise—for he [is] small?”
3 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
YHWH has relented of this, “It will not be,” said YHWH.
4 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
Thus has Lord YHWH showed me, and behold, Lord YHWH is calling to contend by the fire, and it consumes the great deep, indeed, it has consumed the portion, and I say,
5 Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
“Lord YHWH, please cease, How does Jacob arise—for he [is] small?”
6 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
YHWH has relented of this, “It also will not be,” said Lord YHWH.
7 Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
Thus has He showed me, and behold, the Lord is standing by a wall [made according to] a plumb-line, and in His hand a plumb-line;
8 Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
and YHWH says to me, “What are you seeing, Amos?” And I say, “A plumb-line”; and the Lord says: “Behold, I am setting a plumb-line in the midst of My people Israel, I no longer pass over to it.
9 “Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
And high places of Isaac have been desolated, And sanctuaries of Israel are dried up, And I have risen against the house of Jeroboam with a sword.”
10 Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
And Amaziah priest of Beth-El sends to Jeroboam king of Israel, saying, “Amos has conspired against you in the midst of the house of Israel; the land is not able to bear all his words,
11 Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
for thus said Amos: Jeroboam dies by sword, And Israel certainly removes from off its land.”
12 Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
And Amaziah says to Amos, “Seer, go, flee to the land of Judah for yourself, and eat bread there, and there you prophesy;
13 Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
and no longer prophesy [at] Beth-El anymore, for it [is] the king’s sanctuary, and it [is] the royal house.”
14 Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
And Amos answers and says to Amaziah, “I [am] no prophet, nor [am] I a prophet’s son, but I [am] a herdsman, and a cultivator of sycamores,
15 Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
and YHWH takes me from after the flock, and YHWH says to me, Go, prophesy to My people Israel.
16 Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
And now, hear a word of YHWH: You are saying, Do not prophesy against Israel, nor drop [anything] against the house of Isaac,
17 “Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
therefore, thus said YHWH: Your wife goes whoring in the city, And your sons and your daughters fall by sword, And your land is apportioned by line, And you die on an unclean land, And Israel certainly removes from off its land.”

< Amos 7 >