< Amos 7 >

1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
Thus did the Lord Eternal show unto me: and, behold, he was forming locusts in the beginning of the sprouting up of the latter groweth; and, lo, it was the latter growth after the king's mowings [was over].
2 Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
And it came to pass, when they had made an end of eating up the herbs of the earth, that I said, O Lord Eternal, forgive, I beseech thee: how should Jacob be able to endure, since he is so small!
3 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
The Lord bethought himself of this: It shall not be, said the Lord.
4 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
Thus did the Lord Eternal show unto me: and, behold, the Lord Eternal called forth the punishment by fire, and it devoured the great deep, and consumed the ploughed field.
5 Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
Then said I, O Lord Eternal, forbear, I beseech thee: how should Jacob be able to endure, since he is so small!
6 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
The Lord bethought himself of this: Also this shall not be, said the Lord Eternal.
7 Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
Thus he showed unto me: and, behold, the Lord was standing upon a wall [made] by a plumbline, and in his hand was a plumbline.
8 Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
And the Lord said unto me, What dost thou see, 'Amos? And I said, A plumbline. Then said the Lord, Behold, I will set a plumbline in the midst of my people Israel; I will not farther indulge them any more.
9 “Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
And the high places of Isaac shall be made desolate, and the sanctuaries of Israel shall be laid in ruins: and I will rise up against the house of Jerobo'am with the sword.
10 Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
Then sent Amazyah, the priest of Beth-el, to Jerobo'am the king of Israel, saying, 'Amos hath conspired against thee in the midst of the house of Israel: the land is not able to bear all his words.
11 Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
For thus hath 'Amos said, By the sword shall Jerobo'am die, and Israel shall surely be led away into exile out of their own land.
12 Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
And Amazyah said unto 'Amos, Seer, go, flee thee away into the land of Judah, and eat there [thy] bread, and there prophesy;
13 Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
But at Beth-el prophesy not farther any more; for it is the king's sanctuary, and it is a royal residence.
14 Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
Then answered 'Amos, and said to Amazyah, I am no prophet, nor am I a prophet's son; but I am a herdman, and a gatherer of wild figs;
15 Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
But the Lord hath taken me away from behind the flocks, and the Lord said unto me, Go, prophesy unto my people Israel.
16 Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
And now hear thou the word of the Lord, Thou sayest, Prophesy not against Israel, and preach not against the house of Isaac.
17 “Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
Therefore thus hath said the Lord, Thy wife will play the harlot in the city, and thy sons and thy daughters shall fall by the sword, and thy land shall be divided out by the line; and thou shalt die in an unclean land; and Israel shall surely be led forth into exile out of their land.

< Amos 7 >