< Amos 7 >

1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
Thus hath the Lord God shewed vnto mee, and beholde, he formed grashoppers in the beginning of ye shooting vp of the latter grouth: and loe, it was in the latter grouth after the Kings mowing.
2 Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
And when they had made an ende of eating the grasse of the land, then I saide, O Lord God, spare, I beseeche thee: who shall raise vp Iaakob? for he is small.
3 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
So the Lord repented for this. It shall not be, saith the Lord.
4 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
Thus also hath the Lord God shewed vnto me, and behold, the Lord God called to iudgement by fire, and it deuoured the great deepe, and did eate vp a part.
5 Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
Then said I, O Lord God, cease, I beseeche thee: who shall raise vp Iaakob? for he is small.
6 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
So the Lord repented for this. This also shall not be, saith the Lord God.
7 Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
Thus againe he shewed me, and behold, the Lord stoode vpon a wall made by line with a line in his hand.
8 Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
And the Lord saide vnto me, Amos, what seest thou? And I said, A line. Then said the Lord, Beholde, I wil set a line in the middes of my people Israel, and wil passe by them no more.
9 “Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
And the hye places of Izhak shalbe desolate, and the temples of Israel shalbe destroyed: and I wil rise against the house of Ieroboam with the sworde.
10 Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
Then Amaziah the Priest of Beth-el sent to Ieroboam King of Israel, saying, Amos hath conspired against thee in the middes of the house of Israel: the lande is not able to beare all his wordes.
11 Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
For thus Amos saith, Ieroboam shall die by the sworde, and Israel shalbe led away captiue out of their owne land.
12 Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
Also Amaziah sayde vnto Amos, O thou the Seer, goe, flee thou away into the land of Iudah, and there eate thy bread and prophecie there.
13 Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
But prophecie no more at Beth-el: for it is the Kings chappel, and it is the Kings court.
14 Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
Then answered Amos, and said to Amaziah, I was no Prophet, neither was I a prophets sonne, but I was an herdman, and a gatherer of wilde figs.
15 Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
And the Lord tooke me as I followed the flocke, and the Lord said vnto me, Go, prophecie vnto my people Israel.
16 Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
Now therefore heare thou the word of the Lord. Thou sayest, Prophecie not against Israel, and speake nothing against the house of Izhak.
17 “Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
Therefore thus sayth the Lord, Thy wife shall be an harlot in the citie, and thy sonnes and thy daughters shall fall by the sword, and thy land shall be deuided by line: and thou shalt die in a polluted land, and Israel shall surely go into captiuitie forth of his land.

< Amos 7 >