< Amos 7 >

1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
Toto mi ukázal Panovník Hospodin, že aj, formoval kobylky, když nejprvé počala růsti otava, když aj, otava byla po královském posečení.
2 Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
I stalo se, když snědly byliny zemské, že jsem řekl: Panovníče Hospodine, odpustiž, prosím. Kdož zůstane Jákobovi? Neboť ho maličko jest.
3 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
I želel Hospodin toho. Nestaneť se, řekl Hospodin.
4 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
Tedy ukázal mi Panovník Hospodin, a aj, Panovník Hospodin volal, že při svou povede ohněm. A spáliv propast velikou, spálil i díl.
5 Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
Já pak řekl jsem: Panovníče Hospodine, přestaniž, prosím. Kdož zůstane Jákobovi? Neboť ho maličko jest.
6 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
I želel Hospodin toho. A ani toho se nestane, řekl Panovník Hospodin.
7 Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
Potom ukázal mi, a aj, Pán stál na zdi podlé pravidla vzdělané, v jehož ruce bylo pravidlo.
8 Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
I řekl mi Hospodin: Co vidíš, Amose? Řekl jsem: Pravidlo. I řekl Pán: Aj, já položím pravidlo u prostřed lidu svého Izraelského, nebuduť již více promíjeti jemu.
9 “Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
Nebo zpuštěny budou výsosti Izákovy, a svatyně Izraelovy zpustnou, tehdáž, když povstanu proti domu Jeroboámovu s mečem.
10 Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
Tedy poslal Amaziáš kněz Bethelský k Jeroboámovi králi Izraelskému, řka: Spuntoval se proti tobě Amos u prostřed domu Izraelského, ta země nemohla by snésti všech slov jeho.
11 Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
Nebo takto praví Amos: Od meče umře Jeroboám, a Izrael jistotně přestěhován bude z země své.
12 Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
Potom řekl Amaziáš Amosovi: Ó vidoucí, ujdi, radímť, utec do země Judské, a jez tam chléb, a tam prorokuj.
13 Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
Ale v Bethel již více neprorokuj, nebo ono svatyně králova i dům královský jest.
14 Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
Tedy odpovídaje Amos, řekl Amaziášovi: Nebylť jsem já prorokem, ano ani synem prorockým, ale byl jsem skotákem, a česával jsem plané fíky.
15 Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
Ale Hospodin mne vzal, když jsem chodil za stádem, a řekl mi Hospodin: Jdi, prorokuj lidu mému Izraelskému.
16 Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
Nyní tedy slyšiž slovo Hospodinovo. Ty pravíš: Neprorokuj v Izraeli, a nekaž v domě Izákově.
17 “Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
Protož takto praví Hospodin: Žena tvá cizoložiti bude v městě, synové pak tvoji i dcery tvé od meče padnou; a země tvá provazcem dělena bude, a ty v zemi nečisté umřeš, Izrael pak jistotně přestěhován bude z země své.

< Amos 7 >