< Amos 7 >
1 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji yana shirya cincirindon fāri bayan da aka ƙarasa yankan rabon hatsin da yake na sarki, hatsi na biyu kuma yake tohuwa.
Това е, което Госпо Иеова ми показа: - Ето, той образува скакалци, когато отавата почна да никне; и, ето, беше отавата подир царевата коситба.
2 Sa’ad da suka cinye kome, sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ka gafarta! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
И когато скакалците изядоха тревата на земята, тогава рекох: - Господи Иеова, бъди милостив, моля ти се! Как да се издигне Яков? защото е малък.
3 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ba zai faru ba,” in ji Ubangiji.
Господ се разкая за това: Няма да бъде, казва Господ.
4 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya nuna mini. Ubangiji Mai Iko Duka yana shirin hukunta da wuta; wutar ta ƙone teku ta kuma ƙone ƙasa.
Това е, което Господ Иеова ми показа: - Ето Господ Иеова вика на съд чрез огън; и огънят изпояде голямата бездна, и щеше да изпояде и Израилевият дял.
5 Sai na yi kira, na ce, “Ubangiji Mai Iko Duka, ina roƙonka ka dakata! Ta yaya Yaƙub zai tsira? Ga shi ɗan ƙarami ne!”
Тогава рекох: - Господи Иеова, престани, моля ти се! Как да се издигне Яков? защото е малък.
6 Saboda haka sai Ubangiji ya dakatar da nufinsa. “Wannan ma ba zai faru ba,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Господ се разкая за това: И това няма да бъде, казва Господ Иеова.
7 Ga abin da ya nuna mini. Ubangiji yana tsaye kusa da bangon da aka gina, bisa ga awon igiyar gwada gini, da kuma magwaji a hannunsa.
Това е, което ми показа: - Ето, Господ стоеше при стена съградена с отвес, като държеше отвес в ръката си.
8 Sai Ubangiji ya tambaye ni, “Me kake gani, Amos?” Sai na amsa, “Igiyar gwada gini.” Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Duba, zan sa igiyan nan a cikin mutanena Isra’ila; ba zan ƙara barinsu ba.
И Господ ми рече: Що виждаш, Амосе? И рекох - Отвес. Тогава рече Господ: Ето, аз ще туря отвес всред людете си Израиля; Занапред няма вече да ги щадя.
9 “Za a hallakar da wuraren sujada na Ishaku kuma tsarkakan wurare na Isra’ila za su zama kango; da takobina zan tayar wa gidan Yerobowam.”
Високите Исаакови места ще запустеят, И Израилевите светилища ще се съсипят; И аз ще стана с меч против Израилевия дом.
10 Sai Amaziya firist na Betel ya aika da saƙo zuwa wurin Yerobowam sarkin Isra’ila. “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a tsakiyar Isra’ila. Ƙasar ba za tă iya ɗauka abubuwan da yake faɗi ba.
Тогава свещеникът на Ветил Амасия прати до Израилевия цар Иеровоама да кажат: Амос направи заговор против тебе всред Израилевия дом; земята не може да търпи многото му думи.
11 Gama ga abin da Amos yake cewa, “‘Yerobowam zai mutu ta wurin takobi, kuma tabbatacce Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
Защото Амос така казва: Иеровоам ще умре от меч, А Израил непременно ще бъде закаран пленник от земята си.
12 Sai Amaziya ya ce wa Amos, “Tafi daga nan, mai duba kawai! Koma ƙasar Yahuda. Ka nemi abin zaman garinka a can ka kuma yi annabcinka a can.
При това, Амасия, рече на Амоса: О, ти гледачо, иди, бягай в Юдовата земя, там яж хляб, и там пророкувай;
13 Kada ka ƙara yin annabci a Betel, gama nan wuri mai tsarki ne na sarki da kuma haikalin ƙasar.”
а във Ветил вече да не пророкуваш пак, защото е царево светилище, и е царски дворец.
14 Amos ya amsa wa Amaziya, “Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi, amma ni makiyayi ne, kuma ina lura da itatuwan al’ul.
Тогава Амос рече в отговор на Амасия: Не бях аз пророк, нито син на пророк, но бях говедар, и берях черници;
15 Amma Ubangiji ya ɗauke ni daga kiwon dabbobi ya ce mini, ‘Je ka, ka yi wa mutanena Isra’ila annabci.’
а Господ ме взе отподир стадото, и Господ ми рече: Иди пророкувай на людете ми Израиля,
16 Yanzu fa, sai ka ji maganar Ubangiji. Ka ce, “‘Kada in yi annabci a kan Isra’ila, kuma in daina yin wa’azi a kan gidan Ishaku.’
Сега прочее слушай Господнето слово: Ти казваш - Не пророкувай против Израиля, и да не капне от тебе дума против Исааковия дом.
17 “Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “‘Matarka za tă zama karuwa a cikin birni, kuma da takobi za a kashe’ya’yanka maza da mata. Za a auna ƙasarka a kuma raba ta, kai kuma za ka mutu a ƙasar arna. Ba shakka Isra’ila za su tafi zaman bauta, nesa da ainihin ƙasarsu.’”
За това, така казва Господ: - Жена ти ще бъде блудница в града, Синовете ти и дъщерите ти ще паднат от меч, И земята ти ще се раздели с въже; А сам ти ще умреш в нечиста земя, И Израил непременно ще бъде закаран пленник от земята си.